GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Friday 11 May 2012

TAMBAYA TA SITTIN DA DAYA (61) ZUWA TA TAMANIN (80)

61. TAMABAYA

 

Assalamu alaikum warahamatullahi wabara katuh.

Don Allah Malam inaso awarware min wannan rabon gadon.

mamaci ne yabar mahafiyar sa,da yan uwa mata(uwa daya uba daya),sai kuma yan uwa maza da mata(uwa daya uba kowa da nashi)da kakar sa(uwar mahaifinsa).

Shin Malam wadannan zasu iya cinye gadon ko yanuwan mahaifinsa (shakikai)zasu iya shigowa?

Allah yaba Malam ikon amsa tambaya ta.

 

AMSA

Wa alaikum assalam, Za'a

raba abin da ya bari gida:6, a bawa mahaifiyarsa kashi daya, 'yan'uwansa da suka hada uwa kuma kashi biyu, su raba daidai, ragowar kashi ukun sai a bawa 'yan'uwan nasa da suke uwa daya uba daya, duk namiji ya dau rabon mata biyu.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

​​Dr. Jamilu Yusuf Zarewa​​

4/5/2017

 

62. TAMABAYA

ZAN IYA RIKE HANNUN BUDURWATA?

Assalamu alaikum,

Malam Ya Hukunchin Wanda ya rike Hannun wata mace Kuma ba matarsa ba ce, amma Budurwarsa ce?

 

Amsa

Wa alaikumus salam,

 

Bai hallata mutum ya rike hannun wacce ba muharramarsa ba, kuma ba matarsa ta aure ba. Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance ba ya Musafaha (hada hannu) da mata yayin da zai musu mubaya'a, yana yi musu mubaya'a ne da Magana, kamar yadda ya tabbata a hadisi.

Taba hannun budurwa hanya ce da take kaiwa zuwa ga Zina saboda yana tayar da sha'awa, Allah Madaukaki ya haramta kusantar zina a aya ta 32 a suratul Isra'i, Zina tana daga cikin manyan zunuban da babu kamar su bayan shirka da Allah.

Wanda ya kiyaye dokokin Allah, tabbas Allah zai kiyaye shi, wanda ya bı son zuciyarsa, to Allah yana nan a madakata.

 

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

05/05/2016.

 

 

63. TAMABAYA

Assalamu alaikum, Malam tambayata anan macece ta rasu bata haihu ba tana da uwa araye da yaya namiji wanda suke uwa daya uba daya da

Ƙane na miji wanda yake uwa kawai  suka hada da ƙannai mata suma uwa kawai suka hada Allah gafarta malam yaya rabon gado?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Za'a raba abin da ta bari gida :6.

A bawa mahaifiyarta kashi daya, 'yan uwanta da suka hada uwa kashi biyu, sai su raba daidai babu bambanci tsakanin namiji da mace, ragowar kashi ukun sai a bawa dan' uwanta da suke uwa daya uba daya.

 

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

6/05/2017

 

64. TAMABAYA

SHIN ZAN IYA NEMAN SAKI DON MIJINA BAYA HAIHUWA...!!*

Assslam alaika warahamatullah

Dr inada matsala kamar haka fatan za'a taimakamin da amsa malam munyi aure da mijin yau kusan shekara goma muna tare amma Allah bai bamu haihuwa ba sannan kuma dan uwa nane na jini gashi yanzu banason zama dashi shin idan na nemi ya sawwakemin nayi laifi?

Kuma hakan na nuna cewa nakasa cinye jarrabawar da Allah yayimin kenan ?

 

AMSA:

Wassslam Alaiki warahamatullah wabrakatuhu

To yar uwa shi asalin aure a musulunci yana daga cikin manufofinsa shine samun zuri'a ma'ana yaduwa a samu al'ummah

Annabi s.a.w. yace kuyi aure Ku domin Ku samu zuri'a kuma ku auri matayen da kukeso masu haihuwa ni zanyi alfahari da yawanku wajan yawan al'umma ranar alkiyama

To yar uwa bazan ce dake ki rabu dashi ba shawarata gareki shine kiyi hakuri ki yawaita addu'oi wata kila Allah ya baku haihuwar nan gaba amma idan kinga shekarun da kukayi sunyi yawa sunyi miki yawa ba zaki iya cigaba da zama dashi ba bakwa haihuwa zaki iya neman ya sawwake miki amma badon kunyi fada ba kuyi rabuwar lami lafiya to babu laifi shima ya kamata ya sawwake miki amma yar uwa ki sani cewa ba'asan matsalar daga gareki take ba ko daga garesa ne kada sai bayan kun rabu a gane daga gareki ne matsalar

 

Allah shine mafi sani

Dr Abdallah Gadon kaya

 

65. TAMABAYA

LAULAYIN CIKI YASA INA WAIWAYE A SALLAH?

Assalamu alaikum malam Dan Allah macece take fama da yawan zuban yawu a bakinTa na laulayin ciki, Wanda yakai kafun nayi raka'a daya ya cikamun baki sai na dan juya in zuba akan tsumma, sallan yayi ko bani da halin juyawa kadan?

 

Amsa

Wa alaikum assalam. To 'Yar'uwa Annabi s.a.w. yana cewa : "Waiwaye a sallah wani faucewa ne da Shaidan yake fauta daga sallar bawa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lambata : 718.

Malamai suna cewa waiwaye a sallah makaruhi ne saboda hadisin da ya gabata.

Waiwaye yana halatta idan akwai bukata, saboda akwai lokacin da  sayyidina Abubakar ya fara limanci, saboda Annabi s.a.w. baya nan, bayan  Annabi s.a.w. ya dawo sai ya shigo masallaci, sahabbai suna ganinsa sai suka fara tafi, sai sayyadina Abubakar ya waiga lokacin da ya ji tafi ya yi yawa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2544.

Malamai suna cewa : waiwayan da Abubakar ya yi yana nuna hallacin yin waiwaye saboda bukata, tun da Annabi s.a.w. bai masa inkari ba.

Don neman karin bayani duba : Fataawaa nurun Aladdarb 9\225.

A  bisa abin da ya gabata, ya hallata ki dinga yin waiwaye saboda  zubar da yawun da ya zama lalura, saidai duk abin da aka halatta saboda bukata, ba'a so a wuce gwargwadonta .

 

Allah ne mafi sani .

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREAWA

19\4\2015

66. TAMABAYA

HUKUNCIN YIN KIRAN SALLAH BA TARE DA TSARKI BA!

Assalamu Alaikum, malam ko ya halatta mutumin da yake da janaba ya kira sallah?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa wasu daga cikin malamai suna cewa tsarki ba sharadi ba ne yayin kiran sallah, saboda babu wani nassi ingantacce wanda ya nuna hakan, don haka ya halatta ga mai janaba, da mai karamin kari su yi kiran sallah, saidai abin da ya fi shi ne yin cikakken tsarki kafin kiran sallah, saboda fadin Annabi s.a.w " Ina kin na ambaci Allah alhali ba ni da tsarki", kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai lamba ta :16, kuma Albani ya inganta shi a Sahihu-sunani Abi-dawud 1\16.

Don neman Karin bayani duba : Fathul-bary 3\113 da Majmu'u fataawaa wa makaalatin mutanawwi'a 10\338.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

27/6/2015.

 

67. TAMABAYA

INA YAWAN WAYA DA BURDURWATA, KO YA HALATTA A SHARI'ANCE ?

 

Assalamu alaikum malam Dan Allah ina tambaya. Namiji ne yakeso ya qara aure to shine bayan ya dawo gida da dare sai budurwar ta riqa kiran shi ko kuma ta riqa turo txt, shikuma idan matarshi tana kusa sai ya riqa avoiding amma data dan daga sai shima ya fara respinding ko ya kira ta kuma idan asuba tayi sai ta kirashi. To shine matar ba taso, dan Allah a Shari'ance yanada laifi ko ba shi da ? sannan matar zata iya neman ya dena ko kuwa ta shiga rayuwarsa ne a shari'ance ?

 

Amsa:

Wa alaikum assalam To dan'uwa yana da kyau ka san cewa matar da kake nema aure ba muharramarka ba ce, don haka bai halatta ka dinga hira da ita ba, sai gwargwadon bukata.

Yawan hira da budurwa da jin dadin zancenta, yana daga cikin abubuwan da suke kaiwa zuwa ga fitina, mai AHLARI ya kirga jin dadin zancen wacce ba muharrama ba daga cikin ayyukan da Allah ya hana.

Duk wanda yake yawan hira da matar da ba muharramarsa ba, yana jin dadin zancenta, Allah zai iya haramta masa jin dadin zancen matarsa ta halal.

Ya wajaba hirarka da buduwarka ta zama gwargwadon bukata, saboda jin dadin zancenta, zai iya kai ku ku aikata katon sabo, yana daga cikin ka'idojin shari'a toshe duk hanyar da take kaiwa zuwa barna.

Zunubi shi ne abin da ya sosu a ranka kuma ka ji tsoron kar mutane su yi tsinkayo, kamar yadda hakan ya tabbata a hadisin Muslim mai lamba ta: 2553.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR JAMILU YUSUF ZAREWA

4\1\2016.

 

68. TAMABAYA

MAGANIN QARFIN MAZA?

 

Assalamu alaikum, Malam mutum ne yana da chemist yana sayar da magunguna. Ya halatta ya sayar da maganin qarfin maza ga wanda yake so ya biya bukatar iyalinsa? Allah ya qarawa Dr. Jameel imani da lafiya da ilimi, gaskiya muna amfana

 

Amsa:

Wa alaikum assalam, In har an jarraba an samu yana amfani kuma likitoci sun tabbatar ba ya cutarwa ya halatta a siyar da shi don aure ya gyaru, a kara samun donkon soyayya, saboda saduwa tsakanin ma'aurata turke ne tsayayye, wanda in ya goce aure ba zai tafi saiti ba, yana daga cikin ka'idojin Sharia duk harkokin mutane na yau da kullum wadanda ba ibada ba ne sun halatta, in har ba'a samu nassin da ya hana ba.

Addinin musuluci ya haramta duk abin da yake cutarwa, kamar yadda nassoshi masu dinbin yawa suka tabbatar, wannan yasa duk maganin da likitanci ya tabbatar cutarsa ta fi amfaninsa yawa ya wajaba a guje shi, Tunkude cuta ginshike ne a cikin addinin musulunci.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

23/05/2016

 

69. TAMABAYA

MATATA TA YI BARI, AMMA JINI YANA DAUKEWA YA DAWO

Assalamu alaikum, Malam ga wata tambaya a taimakama ,matata ta samu bari to abun bai gama fita ba tana zubar da jini sai ya dauke kwana hudu sai ya dawo sai ta fara sallah sai ya dawo yanzu kusan wata biyu kenan, shin za ta ci gaba da sallah tunda ya zama kamar jinin ciwo?.

 

Amsa

Wa'alaikumus Salaam. Idan mace ta yi barin ciki, to babban abin da za ta lura da shi, shi ne abin da ta yi barin, idan halittar Mutum ta bayyana ga abin da ta yi barin ta yadda za a iya ganin hannu ko kafa da makamancin hakan, to wannan jinin ya zama jinin biki. Don haka sai ta bar Sallah, Azumi, Saduwa da Miji da sauran dukkan abin da aka hana mai biki aikatawa.

Amma idan abin da ta yi bari yana nan a matsayin maniyyi ko gudan jini ko tsokar da babu halittar Mutum a jikinta, to wannan jinin ba jinin biki ba ne, jinin ciwo ne, don haka za ta yi Sallah, Azumi, da sauran duk abin da aka halatta ma mace mai tsarki sai dai duk lokacin da za ta yi sallah, to sai ta yi tsarki ta sake yin Alwala.

Kuma hukuncin jini yana tabbata ne tun daga lokacin da jinin ya fara fitowa koda bata kammala zubar cikin ko haihuwar ba, domin Malaman Musulunci sun hadu akan cewa mace tana iya fara zubar da jinin biki kafin haihuwa indai ta fara nakuda, sai dai Ibn Hazam shi ne yace jinin biki ba zai fara zuwa ba sai mace ta haife dukkan abin da ke cikin cikinta, amma dai tabbatacciyar magana shine: jinin biki yana fara zuba ne a lokacin da Uwa (wadda take fadowa bayan haihuwa a hade da cibin jaririn) ta ballo daga bangon mahaifa.

 

Allah ya bamu ikon ganewa da gyarawa.

 

Amsawa

Malam Ibrahim Jushi

16/05/2017.

 

70. TAMABAYA

DALIBIN DA YA YI AURE DA NIYYAR ŞAKI, IN YA GAMA KARATUNSA?

 

Assalamu alaikum. Malam shin ya halasta mutum yaje karatu wani kasan da Ba nasaba zaiyi shekara 5 sai yayi aure da niyan idan ya gama makarantan nashi sai ya saketa ya koma gida?

 

 

 Amsa:

Wa'alaikum assalam, wasu malaman sun halatta hakan, sai dai zance mafi inganci shi ne rashin halarcinsa, saboda ya yi kama da auran mutu'a, sannan kuma hakan ya sabawa wasu daga cikin manufofin aure. 

Kamar dawwamammar soyayya da kuma debe kewa, Aya ta 21 a suratu Arrum ta tabbatar da cewa: an shar'anta aure ne dön ka nutsu da matar da zaka aura, wannan manufar ta goce a aure da niyyar saki.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

12/05/2016

 

70. TAMABAYA

Da wanda nake so da wanda mahaifiyata ta ke so wazan aura?

 

Malam ina neman shawara inada saurayi me ilimin addini dana buko amma mamana tana sona aure wani mutum mara ilimi kuma ni bana sansa toh malam wazan zaba aciki?

ASSALAMU ALAIKHUM

 

Amsa

Wa'alaiku mussalam, Hadisi ya tabbata wani mutum yazo wajan Annbi S.A.W yace dashi: cikin mutanan duniyannan wanene ya kamta nayi mishi biyayya sai Annabi S.A.W yace dashi: mahaifiyarka ya sake cewa sannan wa? Annabi S.A.W yasake cewa dashi mahaifiyarka, yasake cewa sannan wa? Annabi S.A.W yasake cewa dashi mahaifiyarka, ya sake cewa sannan wa Annabi S.A.W yace mahaifinka.

Muhimmancin hakkin uwa bayan hakkin Allah S.A.W da na Annabi S.A.W babu wanda yafi shi girma daga ita sannan mahaifi, dan haka wajibine bin mahaifiya.

 

Shawara

Ki lallabata har ta gamsu kiyi kokari ta wajan yi mata biyayya da kuma bin kawayanta da yan uwanta cikin ladabi wajan su saka baki dan shawo kanta har Allah yasa ta gamsu ta baki wanda kike so.

Muna Addu'a Allah ya zaba miki wanda yafi Alkhairi.

 

71. TAMABAYA

ZAN IYA DAUKAN AZUMIN NAFILA A JAJIBARIN RAMADAN?

 

Assalamu alaikum

Menene hukuncin wanda keyin azumin litinin da alhamis sai  azumin Ramadan ya kama ranan juma'ah  to ya halasta yayi azumin  ranan  alhamis din Alhalin washe Gari azumin Ramadan?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

In ya saba yi babu laifi ya azumta, saboda hadisin da Annabi S.A.W. yake cewa: " Kada ku gabaci Ramdhana da azumin yini daya ko biyu sai Fa in azumin da mutum ya saba yi ne, kamar yadda Bukhari ya rawaito hakan a hadisi mai lamba ta: 1914 da kuma Muslim a hadisi mai lamba: 1082.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

17/05 /2017

 

72. TAMABAYA

ZAN IYA AURAN 'YAR KANWAR MATATA?

 

Assalamu alaikum Malam, Ya halatta mutum ya auri yar qanwar matarsa?

 

Amsa

Wa alaikum assalam, ya halatta ya aure ta, bayan ya saki matarsa, amma bai halatta ya hada su ba saboda innarta ce, Annabi S.A.W yana cewa: "Ba'a a hada mace da goggonta, ba'a hada mace da innarta a auratayya, saboda in kuka yi haka, za ku lallata zumunci ku" kamar ayadda ibnu Hibban ya rawaito.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

20\5\2016

 

73. TAMABAYA

SANYA ZOBEN AZURFA A DAN YATSAN DAMA?

 

Assalamu Alaikum Malam ga wata tambaya nan kamar haka:Assalam da fatan kana lpy! pls ga tambayana menene hukuncin sa AZURFA ZOBE a hanun dama shin akwai wata illa ne koh kuma manzon Allah baisaba???

 

Amsa

Walaikum assalam.To dan'uwa ya halatta a sanya zoben azurfa a karamin dan yatsan hagu da kuma dama, Nawawy ya hakaito Ijma'in kasancewar hakan Sunna, saidai akwai hadisi mai lamba ta :2078 a Sahihi Muslim wanda yake nuna haramcin sanya zobe a dan yatsan tsakiya da wacce take binta, wasu malaman kuma sun dauki hanin a matsayin karhanci ba haramun ba.

Don neman karin bayani duba Al-majmu'u na Nawawey 4\340.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

28\12\2015

 

74. TAMABAYA

DAN ZINA ZAI GAJI MAHAIFIYARSA?

Assalamu alaykum. Malam don Allah Malam in nada tanbaya, Malam mace ce tayi ciki batare da aure ba, ta haihu kuma tana da kudi sai Allah ya mata rasuwa toh malam yaron zai ci gadonta ?.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

idan mace ta yi cikin shege kuma ta haifi Da, daga baya ta mutu Dan zinar da ta haifa zai gaje ta, saboda Allah madaukakin sarki a cikin suratun Nisa'i aya ta : 10 ya yi wasiyya a bawa 'ya'yaye gado, Dan zina kuma yana cikin jerin 'ya'yayen mahaifiyarsa, wannan yasa zai gaje ta.

Dan zina ba ya gadon mahaifinsa a wajan mafi yawancin malamai, ko da kuwa ya yarda dansa ne.

 

 Allah ne mafi sani

Don neman karin bayani duba : Sunanu Attirmizy hadisi mai lamba ta: 2113 da kuma Tabyinul haka'ik 6\214.

 

Dr. Jamilu Zarewa

25\5\2016

 

75. TAMABAYA

HUKUNCIN AUREN HANNU (Masturbation)

 

Assalmu alaikum, Allah ya kara ma malam lapiya da imani, malam dan Allah menene hukumci masturbation (Istimna'i) a musulunci

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

To 'yar'uwa  Babu nassi ingantacce bayyananne yankakke da yake haramta wasa da al'aura har maniyyi ya fito, duk hadisan da suka zo ba su inganta ba.

Saidai wasu malaman sun haramta auran hannu saboda aya ta 6 a Suratul Muminun ta iyakance biyan bukatar sha'awa ta hanyar matar aure ko bayi kawai, wannan sai ya nuna abin da ba wadannan ba ba'a iya biyan bukata ta hanyar su.

 Yin wasa da al'aura har maniyyi ya fita yana haddasa matsaloli a likitance, saidai yana daga cikin ka'idojin shari'a ; idan cututtuka biyu suka hadu ya zama babu yadda za'a yi sai an aikata daya daga ciki sai a zabi karama a aikata, wannan yasa Imamu Ahmad da Ibnu Hazm suka  halatta auran hannu ga wanda ya ji tsoron zina kuma ba shi da halin da zai yi aure.

Idan mu ka ce auran hannu haramun ne, saidai barnar dake cikin zina tafi girma, domin zina akwai keta alfarma a ciki, sannan tana kaiwa ga cakuduwar nasaba, ta yadda za'a haifi 'ya'ya gantalallu, marasa asali, wannan ya sa magana ta biyu ita ce mafi inganci, mutukar an samu sharudan da suka gabata

Don  neman Karin bayani duba : Muhallah 12\407 da Majmu'ul fataawaa 34\146>

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

23\1\2016

 

76. TAMABAYA

SHIN AKWAI ZAKKA A CIKIN ALBASHI?

 

Assalamu alaikum.Malam yaya zakkar ma'aikaci ya kamata ta zamo? Domin wasu ma'aikatu sukan bada alawus a dunkule wanda ya isa zakkah to amma wasu sukanyi gini ko sayen filaye ko gonaki da kudin kafin shekara ta zagayo sun kare

 

 Amsa

Wa alàikum assalam.To dan'uwa, hukuncin wannan albashi zai fara ne daga lokacin da ya shiga mulkinsa, don haka mutukar ba su shekara ba, to babu zakka a ciki, domin ba kawai samun nisabI ne ya ke wajabta zakka ba, dole sai an samu zagayowar shekara daga lokacin da kudin su ka shiga mulkinsa, don haka duk albashin da ya kai zakka, kuma aka ajjiye shi ya shekara to ya wajaba a fitar masa da zakka, amma mutukar shekara ba ta zagayo masa ba, to zakka ba ta wajaba ba akan wanda ya mallake shi.

Saidai yana daga cikin dabarun da sharia ta haramta, mutum ya yi abin da zai sarayar masa da wajibi da gangan, don haka mutukar ya sayi filayan ne da nufin kaucewa fitar da zakka, to tabbas ya sabawa Allah.

 

Allah ne ma fi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

14/5/2014

 

77. TAMABAYA

HUKUNCIN DILLANCI DA HOTUNAN 'YAMMATA

 

Assalamu alaikum. Malam menene hukuncin 'yan matan da suke bada hotunansu ga tsofafi don su nema musu mijin aure ?

 

AMSA

Wa alaikum assalam Addinin musulunci ya haramta kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, amma ya halatta ka kalli mace, idan kana so ka aure ta, kamar yadda ya zo a cikin hadisi, inda Annabi s.a.w. yake cewa : "Idan dayanku yana neman aure, to in ya sami damar kallon abin da zai kira shi zuwa aurenta, to ya aikata hakan" ABU

DAWUD

Malamai sun yi sabani akan wurin da ya kamata mutum ya kalla a jikin mace lokacin da ya je neman aure :

 

1. Akwai wadanda suka ce zai kalli fuska da tafin hannu ne kawai.

2. Wasu malaman sun tafi akan cewa : zai kalleta a kayan da take sawa a cikin gida, ta fuskace shi ya kalle ta, sannan ta juya baya ya kalleta.

Wannan ra'ayin shi ne ya fi dacewa, saboda ta haka mutum zai san yanayin matar da zai aura.

Ta hanyar bayanan da suka gabata, za mu iya fahimtar cewa aikin dalilin aure ya hallata, amma da sharuda, ga wasu daga ciki :

1. Ya zama hoton ya fito da asalin fuskar matar, bai KWARZANTA ta ba, ta yadda za'a iya yaudarar namijin, ko a rude shi.

2. Ya zama wacce za'a bawa hoton mai amana ce, ta yadda ba za ta nunawa wanda ba shi da nufin aure ba, saboda asali ya haramta ayi kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, sai ga wanda yake nufin aurarta, wannnan yana nuna cewa, bai halatta asa irin wannan hoton na neman aure ba , a face book, ko a jarida.

3. Ka da hoton ya kun shi fito da tsaraici, ya wajaba a tsaya a iya inda shari'a ta bada umarni.

4. Zai fi dacewa ace mace ce za ta yi dalilin aure, saboda in namiji ne, zai iya fitinuwa da hotunan da yake gani, sai barna ta auku, don haka ita ma macen ya wajaba ta ji tsoron Allah a cikin aikinta.

 

Allah shi ne ma fi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

 26/5/2014

 

78. TAMABAYA

KO ZAN IYA BAWA KANNENA ZAKKA?

 

Assalamu alaikum,

Malam ansha ruwa lafi Malam ko ya halatta imba ma'aikatana  zakka da kannena?.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Wa alaikum assalam. To dan'uwa ba ya halatta musulmi ya bada zakka ga wadanda wajibi ne akansa ya ciyar da su; kamar iyaye maza da mata, kakanni; maza da mata, da kuma 'ya'ya da 'ya'yan 'ya'ya ; saboda bada zakka ga wadannan zai sauke masa nauyin ciyar da su da ya ke wajibi akansa; daga nan kuma sai amfanin bada zakkar ta dawo kansa.

Amma kanne kuwa, to ciyar da su bai wajaba akanka ba, don haka ya halatta ka ba su zakka, haka nan ma'aikatanka.

Sannan daga cikin ka'idojin da malamai suke fada a wannan babin shi ne duk mutumin da idan ka mutu ba zai gaje ka ba, to ya halatta ka ba shi zakka, ka ga  kuwa kanne, ba sa gado mutukar akwai 'ya'ya.

Duba fiqhul-muyassar shafi na : 145

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

08/07/2014

 

79. TAMABAYA

MUNA JINKIRTA WANKAN JANABA ZUWA BAYAN ASUBA A WATAN RAMADANA?

 

Assalmu alaikum, malam ina da tambaya shin meye

hukuncin matan da za su sadu da mijinsu lokacin azumi,

amma ba za su yi wanka ba har sai alfijir ya fito, shin yaya

matsayin azumin su yake.? Nagode

 

Amsa

Wa alaikum assalam, ya halatta mace ta sadu da mijinta su

jinkirta wanka zuwa bayan ketowar alfijir a watan

Ramadhana, a zuminsu kuma ya inganta, saboda Annabi

S.a.w yakan yi haka da matansa, kamar yadda iyalansa

A'isha da Ummu Salama suka rawaito hakan, kuma Muslim

ya fitar da riwayar a Sahihinsa a hadisi mai lamba ta: 1874.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

21/05/2016

 

80. TAMABAYA

BANA SO NA SHA AZUMI, KO ZAN IYA SHAN MAGANIN HANA HAILA?

 

Assalamu alaikum,

Allah ya gafarta malam, azumi ya zo ni kuma ba na son na sha ko azumi daya, to shi ne na sayi maganin da zai hanani yin al'ada na sha, bayan mun hadu da kawata, sai take ce min wai babu kyau, shi ne na ce mata ban yarda ba, zan tambayi malamai, don Allah malam a kara min haske ?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa amfani da maganin da yake hana haila ya halatta, Idan ya zama ba zai cutar ba, amma idan zai cutar, to ya haramta saboda fadin Allah “kar ku jefa kawunanku a cikin halaka” suratu Albakarah aya ta 1952. Saidai duk da cewa hakan ya halatta da sharudan da suka gabata, amma barinsa shi ya fi, sai idan bukatar hakan ta taso, saboda mutum ya zauna akan yadda yake ya fi masa kwanciyar hankali akan ya yi abin da zai canza dabi’arsa, musamman ma wasu daga cikin kwayoyin na zamani suna dagula kwanakin haila, kamar yadda ya bayyana gare mu, sai a kiyaye.Don neman karin bayani, duba : Dima'uddabi'iyya shafi na : 54 .

 

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

22\6\2015


No comments: