GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Saturday 12 May 2012

TAMBAYA TA TAMANIN DA DAYA (81) ZUWA TA DARI (100)

81. TAMABAYA

SHIN AMAI NA KARYA AZUMI?

 

Assalamu alaykum'm Malam Dan Allah inada tambaya,nice ina azumi se nayi irin Dan aman nan wanda ake ce masa aman kaji,Dan kadanne ba wae amai da yawaba,to malam ya matsayin azumi na naji ance amai yana karya azumi.Allah y qarawa malam Lpy.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,                 

Duk aman da akayi kadan ko mai yawa ba da gangan ba toh baya karya azumi amma idan

an kakaro shi ne to azumi ya karye, Don fadar manzon Allah cikin hadisin Abu huraira wanda ke cikin sunan na imam tirmizi 720.

Don haka dai babu sabani tsakanin malamai cewa duk wanda amai ya rinjaye shi toh azumin sa na nan amma wanda ya kago amai da kansa to azumin sa ya baci, aduba:

Al'Mugni 4/368

 

Wallahu A'alam

Malam Nuruddeen Muhammad (Mujaheed)

29/05/2017

 

82. TAMABAYA

SUFRA DA KUDRA DA HUKUNCINSU

 

Assalamu alaikum,

Dan Allah Malam Ina bukatar bayani akan "KUDRA da kuma SUFRAH", Allah ya saka da Alkhairi.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa, Wannan yana daga cikin mas'aloli masu mutukar muhimanci, amma ga abin da ya sawwka game da haka :

Sufra na nufin mace ta ga ruwa mai fatsi-fatsi kamar ruwan ciwo, ya fito daga gabanta.

Kudra kuwa na nufin : ruwa ya ringa fitowa daga farjin mace, wanda kalarsa ta ke kasancewa tsakanin fatsi-fatsi da baki wato kamar ruwa gurbatacce,

Dangane da hukuncinsu kuwa : idan daya daga cikinsu ya kasance a tsakiyar haila ne ko kuma yana hade da haila kafin ta sami tsarki to wannan ana saka shi a cikin haila, idan kuma bayan tsarki ne to ba haila ba ne saboda fadin Ummu adiyya mun kasance ba ma kirga sufra da kudra bayan tsarki a cikin haila) Abudawud ya rawaito shi da sanadi mai inganci,

A hadisin A’isha kuma (Mata suna aiko mata da abin da suke sawa lokacin da suke haila a jikinsa akwai sufra (wato ruwan da yake kama da ruwan ciwo) sai ta ce musu kada ku yi gaggawa har sai kun ga farin ruwa ya fito, ta yadda za mu yi amfani da hadisin Ummu adiyya bayan an sami tsarki, ma’ana ko ta ga sufra da kudra ba za ta kirga su a cikin haila ba, hadisin A’isha kuma za mu yi amfani da shi idan tana cikin haila ta yadda za ta kirga da su.

 

ALLAH ne mafi sani.

5/12/2014

Dr Jamilu Zarewa

 

83. TAMABAYA

YA YI WA MATARSA ZIHARI SAI YA SAKE TA KAFIN YA YI KAFFARA?

Assalamu Alaikum, Malam ina da tambaya? Namiji ne ya yi wa matarsa zihari, maimakon ya yi kaffara sai ya sake ta, ya sake wani auren. Malam ya matsayin wannan sakin da matsayin auren?.

 

Allah ya bada ikon isar da wannan sako ga Malam.

 

Amsa:

Wa alaikum assalam, Auransa na biyun ya inganta saboda ba su da alaka da juna.

Wasu Malaman sun tafi akan cewa mutukar saki uku ne, to wancan ziharin ya warware, amma in saki daya ne kuma ya yi kome, to bai halatta ya taba ta har sai ya yi kaffarar ziharin, kamar yadda Ibnu Khudaamah ya fada a cikin Al-Mugni.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr Jamilu Yusuf Zarewa

01/06/2017.

 

84. TAMABAYA

TANA AZUMI SAI MIJINTA YA SUMBACETA?

  

Malam macece tayi kitso alhalin tana azumi sai mijinta yaga kitson ya basa sha'awa saiya sumbacesa ita kuma take sha'awa tazo mata harta jika pant dinta

Wa akaikumus salamTo yar uwa da farko dai anyi wasa da azumi kwarai da gaske kuma ba daidai bane kina azumi ki bari mijinki ya sumbaceki ta yadda har zaki fitar da wani abu dazai bata miki azumi' wannan akwai ganganci a ciki.

Amma shi azumin nafila dama mai shi yanada yan'cin ya karyashi koya cigaba Annabi S.A.W ya fada cikin hadisi sahihi mai azumin nafila shine sarkin kansa idan yaga dama ya karya manzon Allah s.a.w. ya bada wannan damar.

Malamai suna cewa fitar maziyyi idan har maziyyine ya fita karamar sha'awa kenan zance mafi inganci baya karya azumi amma idan maniyyi ne ya fita to azumi ya karye shikenan idan na nafila ne bakida lada idan kuma farilla ne akwai kaffara akansu bisa kaulin malamai amma wasu malaman sukace sai anyi jama'i kaffara take wajabta idan nafilane shikenan idan kuma na farillah ne saiki rama guda daya wannan shine zance mafi inganci.

 

Allah shine mafi sani.

Amsawa

DR. ABDALLAH GADON KAYA

 

85. TAMABAYA

INA CIKIN SADUWA DA MIJINA A RAMADHANA SAI ALFIJIR YA KETO!​​

 

Assalamu alaikum Malam muna cikin saduwa da mijina a cikin wannan wata, sai muka ji kiran sallar asalatu, me ye hukuncin azuminmu?

 

Amsa

Wa alàikum To 'yar'uwa mutukar kuna jin kiran sallar, kun maza da sauri, kun datse saduwar da kuke yi, to azumin ku yana nan, amma in har kuka ci gaba, da yi ko da na second daya ne, to azuminku ya karye, kuma za ku yi kaffara ku duka, idan kin yi masa biyayya, in kuma takura miki ya yi, to zai yi kaffara shi kadai.

Duba Almugni: 3\65.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

DR JAMILU YUSUF ZAREWA

18/06/2015

 

86. TAMABAYA

SHIN ME NENE ZIHARI?

 

Assalamu alaykum Warahmatullahi wabarakatuh. Don Allah Mallam menene ZIHARI? Allah yaqara ilimi mai amfani.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Zihari shi ne mutum ya kamanta matan shi da wata wanda take muharrama a gare Shi kamar Mahaifiyan sa, kanwar shi ko 'Yar shi da ya haifa.

 

Wallahu A'alam

Malam Umar Shehu Zaria

03/03/2017

 

87. TAMABAYA

 

Mata ta mutu ta bar:

1- miji

2- 'Ya'ya mata biyu

3- 'yan-uwa li'abbai Maza da mata

4- 'yan-uwa li'ummai Maza da mata.

 

menene kason kowa

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Za'a raba abin da ta bari gida 12, a bawa mijinta kashi uku, ' ya'yanta mata kashi takwas,  ragowar kashi dayan sai a bawa'  yan'uwa li'abbai su raba.

 

Allah ne mafi sani

4/6/2017

Dr Jamilu Zarewa

88. TAMABAYA

ALAMOMIN KARBAR TUBA

 

Assalamu alaikum dan Allah malam akwai hanyar da mutum yake gane Allah ya yafe masa zunubin da yayi, ya kuma nemi yafiya?

 

Amsa

Wa alaikum assalam.To dan'uwa akwai alamomin da malamai suka fada, wadanda suke nuna Allah ya karbi tuban bawansa, ga wasu daga ciki :

1. Aikata ayyukan alkairi, da son yin abin da zai kusantar da shi zuwa ga Allah.

2. Mutum ya dinga kallon gazawarsa wajan biyayya ga Allah.

3. Ya zama yana yawan girmama zunubin da ya tuba daga shi, yana kuma jin tsoron komawa zuwa gare shi .

4. Ya dinga kallon dacewar da aka ba shi ta tuba, a matsayin ni'ima daga Allah.

5. Ya zama yana yawan nisantar zunubai, sama da kafin ya tuba.

6. Yawan istigfari.

 

7. Son kusantar salihan bayi.

 

Allah ne ma fi sani .   

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA                                                                                5/6/2014

 

89. TAMABAYA

ZAN IYA CIN BASHIN BANKI SABODA ZUWA HAJJI?

 

Assalamu alaikum, malam don Allah ina da tambaya kamar haka - ko zan iya cin bashin banki wato loan domin cika kudin kujerar maka,? Nabiya ma mahaifiyata sabida karin kudin da akayi ya wuce abinda muke zaton cikawa kuma ni ma'aikaciyar gwamnati ce. Na gode Allah yabada ikon amsawa. via UMMUHATUL MUMININ.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

mutukar ba ki da hali to barin zuwa aikin hajjin shi ne daidai,, saboda Allah ya kwashewa kudin ruwa albarka a cikin suratul Bakara kuma ya yi shirin fito-na-fiton yaƙi da wanda ya ci riba,, sannan Allah bai wajabta miki hajji ba ta hanyar bashi,, balle kuma ki biyawa wani.

Hajji yana wajaba ne ga wanda  yake da iko da kuma isasheshen guzirin da zai wadatar da shi daga rokon mutane.

Allah ne mafi sani

5/6/2017

Dr. Jamilu Zarewa

 

90. TAMABAYA

AL'ADATA  TA RIKICE, SABODA SHAN MAGANIN TSARA IYALI ?

 

Assalamu Alaikum Malam don Allah ina da tambaya, don Allah a taimaka min da amsa don kokarin gyara wa Akan lokaci. Malam matsala ta haihuwa greni duk haihuwa ta sai anyi min cs, sai likita ya bani shawarar tsarin iyali don in huta, sai daga nan al'adata Tarikice sai yazo yau bazan sake ganin Shiba sai bayan kwana biyar sai yazo min dayawa, to ni dai wanka na nkeyi nacigaba da ibadata to malam ibadata tayi ko da gyara. Sai kuma da watan Ramadan yazo min dana Kai iya kwankin da yake min wato kwana biyar sai nayi wanka nacigaba da azumi na kuma jinin yana zuwa bai dauke, don sai da yamin wajen kwana goma sannan ya dauke nayi wanka, to shine akace min sai na Rama wannan kwana ki goman shima. To malam ya azumin tawa take.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa Allah madaukakin sarki a cikin alqur'ani ya rataya hukuncin jinin haila ne da samuwarsa, don haka mutukar kin ga jinin haila da siffofinsa (Baki, ko karni) to ya wajaba ki bar  sallah da azumi, har zuwa lokacin da zai dauke, saidai in ya zarce iyaka ta yadda zai zama, yana zubo miki a mafi yawan kwanakin rayuwarki ko dukanta, to a lokacin ne yake zama jinin cuta ta yadda  ba zai hana sallah da azumi ba.

Duk da cewa tsara iyali ya halatta saboda hadisin Jabir wanda yake cewa "Mun kasance muna yin azalo (zubar da maniyyi a waje yayin saduwa) a lokacin da Qur'ani yake sauka, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 4911, saidai  yawancin magungunan tsara iyali suna birkita al'ada, wannan yasa barin su shi ne ya fi, in ba likita ne ya tabbatar da lalurar shan ba, ko kuma aka gane maganin ba ya cutarwa ta hanyar jarrabawa.

 

Allah ne mafi sa ni

Dr. Jamilu Zarewa

22\1\2016

 

91. TAMABAYA

BA A YIN WUTRI BIYU A DARE DAYA?

 

Assalamu alaykum, Malam don Allah Malam amma naji wasu sunce wai idan mutum yayi wuturi a lokacin da ya yi sallan tarawi, toh wai idan zai yi nafila a cikin dare zai kara raka'a daya ya cika wuturin da ya yi da sallah tarawi. shine nake neman karin bayani plxx malam.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Annabi S. A. W. yana cewa ba a wutiri biyu a dare daya, Na'am akwai malaman da suka faɗi siffar da ka ambata, saboda in ka yi hakan zai zamar da waccan ta farkon shafa'i, tun da wutiri daya ake yi a dare.                                       Amma abin da yafi shi ne ko dai barin wutirin tare da liman ko kuma in ka san za ka sake wata sallar daren In liman ya yi sallama kai sai ka tashi ka karo wata raka'ar don ta zama shafa'i kai a wurinka kafin ka yi sallama ,, wannan zai sanya ya zama ba ka yi wutiri ba a lokacin    Annabi S. A. W. yana cewa: "Ku sanya sallarku ta karshe da daddare wutiri".

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Zarewa

07/06/2017.

 

92. TAMABAYA

AURAN KAFURAI BAYAN SUN MUSULUNTA INGANTACCE NE!!

 

Assalamu alaykum, Don Allah ina son a tambaya min malamai wannan tambaya: Wani bawan Allah ne ya musulunta shi da iyalansa ta dalili na, kuma ni na basu kalmar shahada. Su na da yara manya da kanana, sai suka tambaye ni ya ya matsayin auren su nace auren su na nan kamar yadda shariar Musulunci ta tsara, sai yace min to yaya matsayin 'ya'yansu? To gaskiya wannan ne ban sani ba shine nake son a mika min wannan tambaya ga malaman Allah yataimaka ameen.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

To ɗan uwa, auran da kafurai suka yi kafin su musulunta ingantacce ne mutukar sun yi shi akan ƙa'idoji da sharuɗan da suka yarda da su na auratayyarsu, saboda Annabi S. A. W bai canza auran kafiran da suka musulunta ba a zamaninsa, ya tabbatar da su kuma ya yarda da 'ya'yayansu da suka haifa ta hanyar wancan aure.

Sahabban Annabi S. A. W. da yawa an haife su ne ta hanyar auratayyar zamanin maguzanci kuma musulunci ya yarda da dangantakarsu zuwa iyayansu, wannan ya sa duk ɗan da kafurai  suka haifa ta hanyar aure za mu danganta shi zuwa iyayansa bayan sun musulunta.

In kafirai suka yi zina suka haifi Ɗa ba za a danganta shi zuwa babansa ba bayan ya musulunta.

Don neman karin bayani duba: Al-mugni na Ibnu Ƙudama 7/115 da kuma sharhul Mumti'i 12/239.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr Jamilu Yusuf Zarewa

07/06/2017.

 

93. TAMABAYA

SHEKARA DAYA MIJINA BAI SADU DA NI BA, MENENE SHAWARA

 

Assalamu alaykum. Malam ya ibada? Allah yasamu dace. Malam don Allah ina son nasan matsayin aurena shekara daya mijina be kusanceniba alhalin muna tare kuma dukkanin mu muna lafiya. Nagode

 

Amsa

Wa alaikum assalam

 Auranku ingantacce ne, amma zai yi kyau a kira magabatanku a tattauna matsalar, tun da saduwar ma'aurata ginshiki ne na Zamantakewar aure, wanda rashinsa yana kai ma'aurata zuwa saɓon Allah. In har ba ku cimma matsaya ba, bayan zama da magabata kina iya kai shi Kotu alkali ya muku hukunci, Saboda a musulunci bai Halatta miji ya kauracewa matarsa ba sama da wata (4) kamar yadda aya ta (226) a suratul Bakara ta tabbatar da haka.

Allah ne mafi sani

08/06/2017

Dr Jamilu Zarewa

 

94. TAMABAYA

BAMBANCI TSAKANIN MANIYYI DA MAZIYYI DA KUMA WADIYYI

 

 1. Maniyyi

 Maniyyin namiji : ruwa ne mai kauri FARI wanda yake fitowa ya yin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da farji, sannan yana tunkudo juna lokacin da yake fitowa, kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino, ko damammen gari, Idan ya bushe kuma yana yin kamshin kwai.

 

 Maniyyin mace : ruwa ne tsinkakke, MAI FATSI-FATSI, WANI LOKACIN KUMA YANA ZUWA FARI, wanda yake fitowa yayin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da farji, sannan yana tunkudo juna lokacin da yake fitowa, sannan za ta ji tsananin sha'awa da kuma dadi lokacin da ya fito, kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino ko damammen gari, Idan ya bushe kuma yana yin kamshin kwai, kuma za ta ji sha'awarta ta yanke bayan fitowarsa.

HUKUNCINSA SHI NE : YANA WAJABTA WANKA

 2 Maziyyi : Ruwa ne tsinkakke da yake fitowa, yayin karamar sha'awa, kamar tunanin aure ko kuma tuna wacce kake so, ko matarka, ko kallon matar ko namijin da kike sha'awa, haka nan yana fitowa yayin wasa tsakanin miji da mata, saidai shi ba ya sa sha'awa ta tafi, kuma wani lokacin ba'a sanin ya fito.

 Malamai suna cewa : Maziyyi ya fi fitowa mata, fiye da maza, lokacin da maziyyi zai fitowa namiji azzakarinsa zai mike.

 HUKUNCINSA SHI NE A WANKE FARJI GABA DAYA, DA KUMA INDA YA SHAFA, KUMA A SAKE ALWALA

 

 3 Wadiyyi wani ruwa ne mai kauri da yake fitowa a karshen fitsari, ko kuma karshen bahaya ga wanda ya jima bai yi ba, yana fitowa ga wadanda suke fama da gwauranci ko wadanda suka yi nisa da abokin rayuwarsu ta aure, ina nufin namiji ko mace.

 

 YANA DAUKAR DUKA HUKUNCE-HUKUNCEN FITSARI

 

 

Allah ne mafi sani.

31/05/2013

Dr. Jamilu Zarewa.

 

95. TAMABAYA

DAN ACABA ZAI IYA KAI KIRISTA COCI?

Assalamu alaikum, Akramakallahu, Shin ya halatta MUSULMI DAN ACABA ya dauki KIRISTA ya kai Shi COCI, ko ya dauko Shi daga Coci zuwa gida? Domin Suna cewa: Mu Sana'a kawai Mu ke yi, haka abin ya ke a bangaren MAGINA, TELOLI, KAFINTOCI da MA SU WAYARIN da sauran su.

 

Amsa

To dan uwa Allah Madaukakin Sarki Ya hana taimakekeniya wajan aikata sabo, kamar yadda aya ta biyu a suratul Ma'ida ta tabbatar da hakan.

Yana daga cikin sharuddan cinikayya ya zama ta hanyar da shari'a ta yarda, wannan ya sa kafinta da magini ba za su taimaka wajan gina inda za a saba wa Allah ba, ko da kuwa za su samu kudi, kamar yadda bai halatta Tela ya dinka kayan da za a  sanya a coci a kira wanda ba Allah ba.

Duk wanda ya wadatu Allah Zai wadatar da shi, wanda ya kame Allah Zai kamar da shi, Wadatar zuci taska ce da bata karewa.

Don neman Karin bayani duba: Al'umm 4\213. Da kuma Iktidha'u siradil mustakim 2\41.

Allah ne mafi Sani

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

12\2\2016.

 

96. TAMABAYA

DAN ACABA ZAI IYA KAI KIRISTA COCI?

Assalamu alaikum, Akramakallahu, Shin ya halatta MUSULMI DAN ACABA ya dauki KIRISTA ya kai Shi COCI, ko ya dauko Shi daga Coci zuwa gida? Domin Suna cewa: Mu Sana'a kawai Mu ke yi, haka abin ya ke a bangaren MAGINA, TELOLI, KAFINTOCI da MA SU WAYARIN da sauran su.

 

Amsa

To dan uwa Allah Madaukakin Sarki Ya hana taimakekeniya wajan aikata sabo, kamar yadda aya ta biyu a suratul Ma'ida ta tabbatar da hakan.

Yana daga cikin sharuddan cinikayya ya zama ta hanyar da shari'a ta yarda, wannan ya sa kafinta da magini ba za su taimaka wajan gina inda za a saba wa Allah ba, ko da kuwa za su samu kudi, kamar yadda bai halatta Tela ya dinka kayan da za a  sanya a coci a kira wanda ba Allah ba.

Duk wanda ya wadatu Allah Zai wadatar da shi, wanda ya kame Allah Zai kamar da shi, Wadatar zuci taska ce da bata karewa.

Don neman Karin bayani duba: Al'umm 4\213. Da kuma Iktidha'u siradil mustakim 2\41.

 

Allah ne mafi Sani

Amsawa

D.r Jamilu Yusuf Zarewa

12\2\2016.

 

97. TAMABAYA

ZAN IYA DORA RIBA, IDAN AKA WAKILTA NI SAYO ABU?

Assalamu Alaikum Mallam, dan Allah ina da tmby, kaman misalin mutum yana baka kudi ka sayo mishi abu, wataran ya baka kudin ka sayo, wataran kuma sai ka sayo ka kai zai baka kudin, shin koya halasta inci riba a wanda yaban kudinshi in sayo mai, ko kuwa a wanda na sayo da kudina ne kawai zan iyacin riba, banda Wanda ya bada kudinshi? Nagode Allah ya kara basira.

 

Amsa

Allah ya amsa addu'arki 'yar'uwa, idan mutum ya wakilta ki, ya baki kudi ki sayo masa wani abu, bai halatta ki ci riba da shi ba, sai da izininsa, saboda hadisin Urwatu Al-ja'ady lokacin da Annabi s.a.w. ya ba shi dinare (1) don ya sayo masa dabbar layya, sai ya sayo akuyoyi guda biyu, ya sayar da daya akan dinare daya, ya zo ma da Annabi s.a.w. da akuya daya da kuma dinaran da ya aike shi, sai Manzon Allah ya amshe ya yi masa addu'a, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 3642.

Kasancewar Annabi S.a.w. ya tabbatar da shi akan aikinsa, sai ya nuna hakan shi ne shari'a, don haka idan wakili ya samu ragi ko ya ci riba a cinikayyar da aka wakilta shi ya wajaba ya dawo da ita zuwa wanda ya aike shi.

Idan ya wakilta bai bayar da kudi ba, to mutukar kuna kasuwanci a tsakaninku ya halatta a dora riba, amma in ba kwa yin kasuwanci ba za ki dora riba ba, za ki kawo masa abin a kudin da ake siyarwa a kasuwa, saidai in ya bada iznin cin riba, saboda wakili amintacce ne a shari'a, wasu malaman suna ganin za ki iya dora gwargwadon wahalarki, in bai bada kudi ba.

Don neman Karin bayani duba Al-mugni na Ibnu khudaamah 5\86.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

20\1\2016

 

98. TAMABAYA

ZAN IYA HUDA HANCI SABODA KWALLIYA GA MIJINA?

Assalamu'alaikum, Malam don Allah wata ce mijinta ya ce hujin hanci na burge shi. So tana so ta huda sai aka ce mata babu kyau a musulunci. Shin Malam ya abun yake? Haramun ne, ko kuwa tana iya hudawa tasa dankunne ta yi kwalliya da shi?.

 

Amsa

Wa alaikumus Salaam, An tambayi Sheikh Ibnu Uthaimin akan wannan mas' alar ta huda Hancı sai yake cewa: Huda Hancı zai iya zama canza halittar Allah, amma idan Garin da matar da ta huda hancin take ana yın ado a hanci, ta yadda hakan ya zama al'ada, to babu laifi a yi hakan.

Duba: Majmu'u Fatawaa Ibnu Uthaimin 11/137.

Haka nan an tambayi Sheikh Abdul Muhsin Al'abbad akan haka a darasinsa da yake gabatarwa a Haram, sai ya ce babu laifi akan haka.

Bisa Abin da ya gabata ya halatta matar BAHAUSHE ta huda hancinta saboda ta sanya abin kwalliya tun da al'adarsu ce, saboda ya tabbata sahaban Annabi s.a.w mata suna huda kunnansu suna sanya 'yan kunnaye Kamar yadda hadisin Bukhari mai lamba: 98 yake nuni zuwa hakan.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

4\1\2016.

 

99. TAMABAYA

ZAN IYA JAN  CARBI, KO KO BIDI'A NE ?

 

Assalamu Alaikum. Tambaya. Allah ya gafartawa Malam Na kasance ina amfani da charbi (Tasbaha) domin yana tunatar dani wajen ambaton Allah a kowane lokaci. Ina matsayin haka a sharia?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa jan carbi ba bidi'a ba ne, saboda duk da cewa babu shi a zamanin Annabi s.a.w. hakan ba zai sa ya  zama bidi'a ba, saboda wanda yake amfani da shi ba ya nufin cewa ibada ce mai zaman kanta, yana amfani da shi ne, don ya kiyaye adadin zikirinsa.

Yin amfani da 'yan yatsu shi ne yafi, saboda hadisi ya yi nuni cewa : za'a ba su dama su yi magana, ranar alkiyama, kamar yadda Tirmizi ya rawaito kuma Albani ya inganta shi a hadisi mai lamba ta: 3486,  don haka za su yi maka shaidar abin da ka yi na alkairi, sabanin carbi.

Sannan sau da yawa za ka ga mutum yana jan carbi amma hankalisa yana wani wajen, sabanin idan da hannu yake yi.

Jan carbi yakan iya sanya wasu su yi riya, saboda wasu suna ratayawa ne a wuya don a gane su zakirai ne.

Annabi s.aw. yana yin tasbihi da hannunsa na dama kamar yadda ya tabbata a hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 1286, wanda Albani ya inganta, saidai wasu malaman suna cewa in ya yi da hagu ma yayi, tare da cewa yi da dama shi ne yafi.

Saidai duk da dalilan da suka gabata, mutum zai iya jan carbinsa, tun da jan carbi ba ibada ce mai zaman kanta ba, balle ace ya zama bidi'a, ga shi kuma ba'a samu wani hadisi da ya hana ba, tare da cewa yi da hannu shi ne yafi.

Don neman Karin bayani duba : Majmu'ul fataawa  22\187. da Lika'ul maftuh na Ibnu-uthaimin 3\30.

 

 Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

24\3\2015

 

100. TAMABAYA

Ya ya wannan rabon gadon yake?

 

Assalamu alaikum. Allah ya karama dr lafiya.mlm dan Allah yaya rabin gadon mutumin da ya rasu ya bar 'ya'ya 24 maza 14 amman daya arnene. Mata 10. da matanshi biyu. dr yaya rabon gadon su yake?? kuma dr rabon gado dole ne a musulunci

 

Amsa

Wa  alaikum assalam,

 za'a raba  abin  da ya bari gida:8, a bawa  matansa kashi  daya  su raba, ragowar  kashi  bakwan  Sai a bawa  'ya'yansa (23) su  raba, duk  namiji ya  dau  rabon   mata  biyu.

Ba za'a  bawa  dansa  kafuri ba, Domin Arne  ba ya  gadon  musulmi saboda  hadisin  Annabi  S. A. W da ya tabbata akan  haka.

Allah ne  mafi  Sani.

 

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

16/06/2017


No comments: