GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Wednesday 19 October 2011

TAMBAYA TA ARBA'IN (41) DA DAYA ZUWA TA SITTIN (60)

41. TAMBAYA

LARABGANA A WATAN SAFAR?

 

Assalamu alaikum mallam tambayana shine naji wasu mutane suna yin wani sallah yau, raka'a hudu wai sunan sallar LARABGANA Ena so dan allah mallam yamin bayanin sallar?

                           

Amsa

Wa alaikum assalam, To dan'unwa yana dağa cikin bidi'o'in zamanın maguzanci kudirta cewa

larabar karşhen watan Safar tana kunshe da bala'oi, addinin musulunci ya  karya wannan camfin bayan zuwan Annabi S.A.W. don haka watan safar daya ne dağa çıkın watanni 12 wadanda Allah ya tabbatar, bai kebanta da wani bala'i na musamman ba.           

  Babu wata aya ko hadisi da ya kebance larabar karshen watan Safar da wata ibada ta musamman, don haka yın nafilfili saboda neman kariya dağa musifun LARABGANA, na daga çıkın bidi'o'i da ba su da asali a musulunci.         

 Don neman karın bayani duba Fatawa a Alajnah Adda'imah 2/354. Allah ne mafi sani.

 

Amsawa:

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

9/12/2015.

 

42. TAMBAYA

FITINTINU SUN MANA YAWA, GA KUMA FIRGICI, MENENE MAFITA?

 

Assalamu Alaykum Akaramakallah, da fatan rubutuna zai zo maka cikin koshin lafiya. In cikin matsala da jarabawa kusan shekara biyu yanzu. Na farko, na dauko wata yarinya na riko, ta gamu da aljanu, ta koma gida, da zata dawo, ta dawo da jan kaya wai ta sa ajikinta duk ranar lahadi, wai ta samu sauki. Maigida na ya hanata sa kayan. Bayan kamar wata biyu, muka fita kasuwa, dukammu muka fita kasuwa sayayya, maigida na ya ga pilowa ya saya, bayan hakan muka fara ganin gashin tsuntsaye a gida. duk lokacin da karenmu yayi kuka sosai, tabbas zamu kwashe gashin da yawa a gida ranar. Muka shiga addu'a da karanta alquran cikin gida. Yarana uku duk yammata, duk safiyan Allah za su tashi da idanunsu jawur, da maigidana. Ni kuma, ina cikin yin azkar dare da rana, abunda suka sa min shine firgita da tsoro, a duk lokacin da karenmu ya fara kuka ko da rana ko da dare, sai in kama firgita sosai da kuma ganin wadanan gashin. Mu na nan da haka, Allah ya nuna mamu pilowan nan da muka saya gashi ne cike da ita. Muka kone ta. Bayan haka ne damuwan ya karu. Gashinne cikin kayan sawanmu, da na yara, karkashin gadonmu da na yara na, akan gado, cikin mota ne ko ina agida attah net na windodin mu, har ata abincinmu. Muka bar gidan, inda muka koma, suka biyo mu, kuma duk lokacin da muka shiga kauyenmu, sai su biyo mu gidan kauye. Ayanzu dai haka, muna sabon gida, kuma sunanan da mu, akan kujerunmu, cikin net na windodin gida ne, gashin na nan. Yanzu ma ciki gareni na wata shidda. Duk magungunan da zikirkiri na sunnah, muna tayi, yarinya mai aljanin kuma har yanzu suna nan da ita, sun sha yin alkawari zasu fita amma ba su fitaba, yanmata ne musulmai ajikinta. Ba kuma wanda zai iya gaya mana ga abunda ke damumu. Mun sha magunguna da na wanka, da hayakin mun gaji. Yanzu dai har, na bar duk magungun, amma ban bar yin addu'a ba. Akaramakallah, ko za'a iya taimaka min da addu'a ko shawaran bi na samu maganin abubawan da Ikon Allah anan. Allah ya saka da alkhairi..

 

Amsa

Wa alaikum assalam

To 'yar'uwa tabbas ba a warware sihiri ta hanyar sihiri, saidai ana iya warware sihiri ta hanyar ayoyin Alqur'ani, wasu malaman sun yi bayani cewa : ana iya warware sihiri ta hanyar karanta Ayatul-kursiyyu da Kuliya da Iklas da Falaki da Nasi, da kuma aya ta : 117 zuwa ta 122, na suratul A'araf, sai kuma aya ta : 79-81 a suratu Yunus, sannan sai a hada da aya ta : 65-70 a suratu Dhaha, za'a karanta su, sai a tofa a ruwan da aka zuba magarya guda bakwai.

Sannan ina yi miki wasici da yawan karatun suratul Bakara,saboda muhimmancinta wajan kore shaidanu, kamar yadda ya tabbata a hadisi, kada ki manta da karanta addu'o'in shiga bandaki da na bacci, da azkar na safe da yamma, da kuma tuba daga zunubai, saboda wasu musifun zunubai su ke kawo su.

Idan fitintinun suka cigaba za ku iya mayar da 'yar rikon, saboda zai iya yiwuwa a tare da ita shu'umcin yake, tun da a baya ba ku ga haka ba, yana daga cikin ka'idojin sharia, ana tunkude cutar da ta shafi mutane da yawa ta hanyar kau da kai akan cutar da za ta shafi mutum daya, wannan ya sa mayar da ita bai zai zama laifi ba.

Yana daga cikin hanyoyin tunkude fititinu, nisantar dukiyar haram, in har a kayan gidan da kuke ciki akwai dukiyar da kuka mallaka ta hanyar haram ya wajaba a fitar da ita zuwa mai ita.                         

                                                                                                Yin sadaka da taimakawa musulmi yana warware mushkiloli, saboda duk wanda ya yayewa wani bakin ciki, Allah zai duba dumuwarsa, hakura da wancan shaidanin karen na ku yana da muhimmanci, saboda mala'iku ba sa shiga cikin gidan da yake akwai kare, kamar yadda ya tabbata a hadisin Bukhari.                                                      In har kin bi wadannan shawarwari ina ga za ki samu nasara mai girma.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa:

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

7\2\2016.

 

43. TAMBAYA

MACE ZA TA IYA BAWA MIJINTA ZAKKA ?*

 

Assalamu alaikum. Malam Menene sahihi akan mace tabawa mijnta zakkah?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

ya halatta a zancen mafi yawan malamai saboda hadisin Zainab matar Abdullahi Dan Mas'ud wanda Bukhari ya rawaito a   sahihinsa a lamba ta:(1462) da kuma Muslim a hadisi mai lamba ta: (1000) lokacin da ta nemi fatwa akan bawa mijinta sadaka kuma Annabi S A W. ya halatta mata hakan.

Malaman sun kafa hujja da wannan hadisin saboda kalmar sadaka ta kunshi farilla da sunna  .

Aya ta (60) a suratu Attaubah ta yi bayanin nau'o'i takwas na mutanen da ake bawa zakka, daga ciki akwai talaka, hakan sai ya nuna mutukar miji talaka ne matarsa za ta iya ba shi zakka, tun da ba'a samu dalilin da ya fitar da shi ba.

 

Saidai Ibnul Munzir ya hakaito ijma'i cewa: "Bai halatta miji ya bawa matarsa zakka ba idan tana fama da talauci, tun da zai iya wadatata ta hanyar ciyarwar da Allah ya wajabta masa.

 

Don neman karin bayani duba: Sharhul Mumti'i (6/168) da kuma Fataawa Allajnah Adda'imah (10/62)

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

21/11 /2017

 

44. TAMBAYA

HUKUNCIN RUFE MUSULMI HADE DA ARNA!

Assalamu Alaikum. Dr muna son karin hasken shari'ar Musulunci akan yadda sojoji ke  bikin karrama matansu da kuma yadda suke rufe Musulmi da wadanda ba musulmi ba a makabarta daya.?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

malaman musulunci suna cewa: Ba'a rufe MUSULMAI da kafirai a makabarta daya kuma hakan shi ne aikin magabata tun zamanin Annabi s.a.w, har zuwa yau daga cikin dalilai akan haka shi ne manzon Allah S.A.W. ya wuce makabartar kafirai sai ya ce wadannan alkairi ya rigaye su, da kuma ya wuce makabartar musulmai sai ya ce wadannan sharri ya rigaye su kamar yadda Nisa'i ya rawaito, wannan sai ya nuna banbanci tsakanin makabartun biyu.

 

 Idan aka rufe musulmi a makabartar kafirai in an yi musu azaba za ta same shi, saboda aya ta: 46 a suratu Gafir ta nuna ana yi musu azaba a kabarinsu.

 

Yin bukukuwa yayin bunne musulmi ya sabawa ka'idojin SHARIA sanannu, don haka ya kamata musulmi su jarraba amsar gawarsu mutukar hakan zai yiwu.

 

Allah ne mafi sani.

 

Don neman Karin bayani duba Al-mugni na Ibnu-khudaamah 2/563

Amsawa: Dr. JAMILU ZAREWA

21/11/2016

 

45. TAMBAYA

MIJINA BA YA BIYA MIN BUKATA, MENENE SHAWARA ?

 

Assalamun alaikum, Malam mace ce mijinta ba ya iya biya mata bukata saboda raunin mazakutarsa, kuma ashe abin da ya raba shi da uwar gidansa kenan.

Kasancewar ba ya biya mata bukata ta shiga cikin halin damuwa, sannan ta yanke shawarar cewa: in ya kira ta shimfidarsa ta daina zuwa, to malam ta yi laifi game da wannan shawarar da ta yanke ?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

A shawarata kamata yayi a kira magabatansu su xauna su tattauna a gano yadda xa'a warware matsalar.

Idan har ya tabbata ba cikakken namiji ba ne to xa'a bashi shekara daya ya nemo magani.

Idan ya warke shikenan, in bai warke ba kuma xa ta iya fadawa cikin haram idan taci gaba da xama dashi, to ya halarta a raba auran, kamar yadda aka raba da uwar gidan.

Yana daga cikin manyan manufofin aure: ma'aurata guda biyu su katange junansu daga haram, in har aka rasa wannan to akwai matsala a xamantakewar aure.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

22/11/2017

 

46. TAMBAYA

BA KOWACCE "ALLAH YA ISA" TAKE TASIRI BA!

                      

Assalamu Alaikum, Allah Ya Gafarta Malam, Uba Ne A Cikin Gida Duk Hakkokin Dake Kan Shi Na Iyalan Shi Baya Saukewa, Sai Matar Ce Take yin Komai, Kama Daga Cin Yara, Suturar Su, Dawainiyar Makaranta Da Sauran Su, Sai Rannan Wata Yar Hatsaniya Ta Shiga Tsakanin Su, Sai Yace Duk Abunda Ta Kara yi A Gidan Wanda Yake Hakkin Shi Ne Allah Ya Isa Bai Yafe Mata Ba, Kuma Malam, Bayyi Idan Ta Bari Yayan Ta Zasu Galabaita Su Shiga Ukku, To Malam Idan Taci Gaba Dayi Allah Ya Isan Shi Zata Bi Ta? Nagode   

            

Amsa                                                                                                                      Wa alaikum as salam,

Ya wajaba ya ciyar da su, in kuma ya kı sai ta Kai shi wajan alkali, tun da ciyar da iyalai wajibı ne akan Uba mutukar yana da iko, Hindu bintu Utbah ta je wajan  Annabi s.a.w. ta fada masa cewa: mijinta Abu Sufyan marowaci ne ba ya bata abin da zai ishe ta, ita da iyalanta, sai Annabi s.a.w. ya ce mata : Ki dauki abin da zai işhe ki ke da yaranki dağa dukiyarsa. Buhari ne ya rawaito.

Idan kuma ba shi da hali kina iya ciyar da su, "ALLAH YA ISAN SHI" ba za ta cutar da ke ba, saboda ba kowacce adduar sharri Allah yake amsa ba, ında Allah yana amsar dükkan addu'o'in sharrin da mutane suke yi, da sun hallaka sun kare, kamar yadda aya ta : 11  a suratu Yunus take nuni zuwa hakan.

                                                                                                                     Allah ne mafi Sani 

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa                                                                       20/11/2015

 

47. TAMBAYA

INA SO NA YI TSAYUWAR DARE, AMMMA NA GAZA?

 

Assalamu Alaikum

Malam ina sha'awar yin tsayuwar dare saboda dimbin falalar da ta kunsa, saidai a lokuta da yawa, na kan so na tashi, amma sai na kasa, ko malam zai taimaka min da shawarwari akan abin da zai taimake ni wajan yin wannan babban aikin, Allah ya karawa malam daukaka, amin.

 

Amsa

Wa'alaikum assalam.

To dan'uwa ina fatan Allah ya datar da mu gaba daya zuwa wannan ibada mai girma, akwai abubuwa da malamai suka yi bayanin cewa, suna taimakawa wajan samun damar tsayuwar dare,  ga wasu daga ciki :

 

1. Baccin rana : Hasanul Basary ya wuce wasu mutane a kasuwa da rana, sai ya ce wadannan ba za su yi bacci ba, sai aka ce masa E, sai  ya ce ina ganin darensu ba zai yi kyau ba" .

 

2. Yin bacci da wuri , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya karhanta bacci kafin sallar isha da kuma yin hira bayanta, kamar yadda ya zo a hadisin Muslim mai lamba ta : 647, kuma dalilin da ya sa ya karhanta hin hira bayanta saboda hakan zai iya hana mutum tsayuwar dare.

 

3. Aikata ladubban bacci yayin kwanciya, ta yadda zai karanta abin da ya zo a cikin sunna na ladubban bacci.

 

4. Umartar wani ya tashe shi kamar matarsa ko wanda suke tare.

 

5. Rashin cika ciki da abinci.

 

6. Nisantar yin aiki mai wahala da rana.

 

7. Nisantar abin da zai kawo maka fargaba a cikin zuciya, ta hanyar rage burirrika da tunanin abin da ya wuce

 

8. Nisantar zunubai, Fudhail bn Iyadh yana cewa : "idan ka ga ba ka iya tsayuwar dare, to ka tabbatar zunubai ne suka dabaibaye ka

 

ALLAH NE MA FI SANI

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

25/11/2014

 

48. TAMBAYA

TSINTUWAR DA AKE YIMA CIGIYA?

                                                                                                          Assalamu alaikum

Malam wani bawan Allah ne ya tsinci Naira: #500#,  a wurin kuma bai ga wadanda zai yi wa cikiya ba...  Ya ya kamata yayi da kudin tsintuwar?,  suna ajiye yanzu haka kusan wata daya .

 

Amsa                                                                                                                                                                 Wa alakum assalam

To dan'uwa idan mutum ya yi tsintuwa ya wajaba a gare shi ya yi cigiya har tsawon shekara guda, idan bai samu mai ita ba, daga nan zai iya amfani da ita, amma in mai ita ya zo daga baya zai biya shi, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 5761.                                                                                     Amma idan abin da ya tsinta dan kadan ne ba shi da yawa, to ya halatta ya yi amfani da shi ko da bai yi cigiya ba, saboda abin da aka rawaito cewa : Annabi s.a.w. ya ga wani dabino akan hanya, sai ya ce : In ban da ına tsoron na sadaka ne da na ci. Muslim ya rawaito a lamba ta:2527,  sai hadişin ya nuna dan karamin abu ba ya bukatar cigiya. 

 

Malamai şun yi sabani wajan iyakance tsintuwar da ba ta bukatar cigiya, wasu sun ce za'a koma al'adar mutane, duk abin da mutane şuke ganinsa ba a bakin komai ba, to in an  tsince shi ba ya bukatar cigiya, Ibnu Khudama ya hakaito daga Imamu Malik cewa: bai wajaba mutum ya yi cigiyar  abin da bai Kai a yanke hannu saboda shi ba, wato daya bisa hudun dinari, haka nan sayyadina Aliyu ya tsinci dinare daya ya yi amfani da ita ba tare da yayi cigiya ba.                                                      Abin da ya gabata yana nuna cewa: mutukar ba ka samu mai Naira (5,00) din da ka tsinta ba a kusa da Kai, ya halatta ka yi amfani da ita ba tare da cigiya ba, tun ba kudi ne mai yawa ba, kuma mai ita ba zai kwallafa rai Akanta ba.

                                                                                    Don neman karin bayani duba : Al-mugni 6/351.

                                                                        Allah ne mafi Sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

1/11/2015

 

49. TAMBAYA

ZAN IYA SADUWA DA MAI HAILA, IDAN NA SANYA CONDOM?

Assalamu Alaikum. Malam Allah ya karama daukaka da imani. Ga tambayata: Shin mutum zai iya saduwa da matarsa idan tana Haila matukar yasa Condom?

 

Amsa

Wa'alaikum assalam. 

To dan'uwa bai halatta ka sadu da mai haila ba ko da kuwa ka sanya Condum, saboda Allah ya haramta saduwa da mai haila, kuma ya kira jinin haila a aya ta 222 a suratul. Bakara da cuta, sannan ya rataya halaccin saduwa da mace mai haila da abubuwa biyu wato: yankewar jini da kuma yın wanka.                                                      

Ba namiji ne kadai haila take iya cutarwa ba, idan ana saduwa da mace mai haila mahaifarta za ta takure sai jini ya barke mata, wannan sai yake nuna cewa: ba za'a sadu da mace mai haila ba ko da an sa Condum .

          

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

28/11/2015

 

50. TAMBAYA

SAFARAR JAKUNA ZUWA GA ARNA!

 

Assalamu Alaikum

Dr. Barka da dare dafatan kunwuni lafiya Dr. Mutanenmu musulmai suna kaiwa arna jakuna suna ci. Menene hukuncin dillalai da masu sayarwa da masu saye su kai da direbobin da suke kaiwa da sauran ma'aikata a cikin harkar?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

A zahirin nassoshin sharia, yin hakan taimakekeniya ne wajan aikata zunubi, Don haka dukkansu sun aikata haramun, tunda Annabi s.a.w. ya haramta cin jakin gida ranar yakin Khaibar.

Siyarwa Wanda aka tabbatar zai ci taimaka masa ne wajan sabawa sharia, wanda ya kiyaye Allah zai kiyaye shi, Wanda ya keta dokokinsa zai same shi a madakata.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

30/11/2016



51. TAMABAYA

 SHIN MACE NA IYA BIN SALLAN JANA IZA?

Assalamu alaikum ,malam menene halaccin bin mata sallar jana iza?Allah yasakada alkairi.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam Warahmatullahi wa barakaatuhu,

Sheikh Abdulaziz Bn Baz yana cewa:

Sallan janaza an shar'anta ta ga maza da mata saboda fadin Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama:

"Duk wanda ya halarci sallan janaza har aka yi mata salla, to yana da kiraadi daya, wanda kuma ya halarci sallan kuma har aka rufe ta tare da shi, to yana da kiraadi guda biyu” sai aka ce mene ne kiraadi guda biyu?, sai ya ce: "misalin manyan dutsawu guda biyu”. Yana nufin wurin lada da za a bashi. Bukhari da Muslim suka riwaito.

Sai dai ba a halasta ma mata su bi janaza zuwa makabarta ba, saboda hadisin Ummu Adiyyah wanda ya tabbata a cikin Bukhari da Muslim take cewa: “An hana mu, mu bi gawa zuwa makabarta...”.

Domin neman karin bayani a duba Majmu' Fataawaa na Sheikh Bn Baz (13/134).

Wannan kuma ita Fatawar Sheikh Muhammad Salih al-Uthaimeen, Allah Ta'ala Ya yi musu rahama baki daya.

Wallahu A'alam

Amsawa:

Malam umar shehu Zaria

26 /04 /2017

 

52. TAMABAYA

ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SAMUN ILIMIN ADDINI

Assalamu alaikum

Akaramukallahu Allah ya kara basira, kuma ina neman shawara cewa ni ina son na yi karatun addini, amma da na fara sai na ji kamar raina ba ya so, a bani shawara nagode.

 

Amsa :

Wa alaikum assalam.To dan'uwa akwai abubuwan da suke taimakawa wajan samun ilimin addini, ga muhimmai daga cikinsu :

 

1. Tsarkake niyya- duk lokacin da ka tsarkake niyyarka wajan neman ilimi, to Allah zai taimakeka.

2. Yin aiki da abin da mutum ya karanta- domin yin aiki da ilimi yana daga cikin abubuwan da suke taimakawa wurin rike ilimi da kuma kiyaye shi.

3. Neman taimakon Allah – saboda ana so mai neman ilimi ya dinga tunawa cewa Allah shi ne MASANI mai sanar da kowa, don haka ya dinga neman taimako a wurinsa yana rokonsa ya buda masa basira.

4. Nisantar zunubai, saboda ilimin addini haske ne, kuma hasken Allah ba ya bawa mai sabo.

5. Yawan maimaitawa, domin maimaita ilimi na daga cikin abubuwan da suke taimakawa wajan samun ilimi da tabbatarsa a zukata .

6. Jure wahala da kuma hakuri , saboda neman ilimi ba ya yiwuwa sai da wahala kuma duk wanda ba zai iya jure wahala ba, zai yi wuya ya iya neman ilimi yadda ya kamata.

7. . Farawa da abin da ya dace da dalibi, domin ana so dalibi ya fara da littafin da ya dace da shi wurin neman ilimi, saboda idan ya fara da littafin da ya wuce matakin karatunsa, ba zai fahimce ba.

 

Ina tabbatar maka mutukar ka rike wadannan to Allah zai taimakeka, ka samu ilimi cikin kwanciyar hankali

 

 Allah ne mafi sani

 

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

26/4/2014

 

53. TAMABAYA

WURAREN DA YA HALATTA A SAKI MACE MAI HAILA !

Assalamu alaikum.

Akaramakallah na ji an ce haramun ne a saki mace mai haila, to amma wani lokacin za ka ga kun samu rashin jituwa da matarka ta yadda ba za ka iya jiran lokacin tsarkinta ba, to malam ko akwai wasu lokuta ne da aka halattawa mutum ya saki matarsa ko da tana haila ?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 

To dan'uwa tabbas Allah ya yi umarni da kar a saki mace sai tana da tsarki kamar yadda yake cewa "Idan za ku saki mata to Ku sake su a farkon iddarsu) ma'ana a tsarkin da ba ku take su ba, Addalak aya ta : (1) saidai akwai wurare guda hudu da ya halattta a saki mace mai haila :

 

1.Idan sakin ya kasance kafin ya kadaita da ita ko kafin ya sadu da ita, to anan ya halatta ya sake ta tana haila.

2. Idan ta yi hailar ne tana da ciki.

3. idan ya sake ta ne bayan ta fanshi kanta, to anan ya halatta ko da tana haila, saboda Annabi s.a.w. bai tambayi matar Thabit ba shin tana haila ne ko tana da tsarki, lokacin da zata yiwa mijinta kul'i, kamar yadda Bhukari ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 5273.

4. Idan watanni hudu suka cika a lokacin ila'i, to ko da tana haila zai iya sakinta.

Don neman karin bayani duba : Dima'uddaabi'iyya shafi na :33

 

In ban da wadannan wurare, to bai halatta a saki mai haila ba, kuma yin har an sake ta, to sakin bai auku ba a wajen wasu malaman.

Allah ne mafi sani.

 

Dr.Jamilu Zarawa

27/4/2014

 

54. TAMABAYA

SHIN BAIKO AURE NE?

Assalamu alaikum,

Malam an yi min baiko da wani mutum, to shi ne zai yi tafiya sai ya biyo ta gidanmu wai yana so mu sadu, ya yi ta kawo min kauli-da-ba'adi, akan cewa, ai mun riga mun yi aure, ni dai gaskiya malam na ki yarda saboda ina da shakka akai, shi ne nake neman fatawa ?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 

To 'yar'uwa tabbas akwai malaman da suka yi fatawa a Nigeria cewa : baiko aure ne, saidai zance mafi inganci shi ne baiko ba aure ba ne saboda hujjoji kamar haka :

 

1. Abin da aka sani shi ne kudin da ake bayarwa yayin baiko ba'a bada su da nufin sadaki, duk da cewa wasu suna dunkulewa su bayar gaba daya, kin ga kuwa in haka ne, to ai dukkan aiyuka ba sa ingatuwa sai da niyya, kamar yadda ya zo a hadisni da dukkan malaman hadisi suka rawaito.

2. Bayan an yi baiko mutum zai iya cewa ya fasa, a dawo masa da kudinsa, kin ga wannan yana nuna ba aure ba ne.

3. Hakan zai iya bude hanyoyin barna, don dukkan wani ashararu zai iya kai kudi a yi masa baiko da wacce yake so ya yi lalata da ita, addinin musulunci kuma ya haramta duk abin da yake kaiwa zuwa barna.

4. Yana daga cikin sharudan auren a wajan wasu malaman samun shaidu, kin ga kuwa wani lokacin wanda zai kai kudin da za'a yi baiko, zai iya zama mutum daya, kin ga akwai nakasu kenan.

5. Abin da muka sani a kasar Hausa, sai bayan an yi baiko, ake sanya ranar daurin aure, kin ga wannann yana nuna cewa, baiko daban, aure daban.

6. Sannan duk  mun yarda cewa baiko ba ya wajabta gado  tsakanin wadanda aka yiwa, idan daya daga cikinsu ya mutu  kin ga wannan yana nuna cewa ba aure ba ne, domin ma'aurata suna gadon junansu.

Allah ne mafi sani .

Dr. Jamilu Zarewa

24/3/2014

55. TAMABAYA

BAMBANCI TSAKANIN RIIBA DA RIBA

Assalamu alaikum, malam

Don Allah ina da tambaya? wai miye riba a musulunci? kuma idan mutum ya siyi abu nera 5 ya halatta ya sai da akan nera 8?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 

To malama riba ta kasu kashi biyu :

 

1. Akwai ribar jinkiri, kamar ka ba mutum bashin naira hamsin, ka nemi ya dawo maka da naira sittin, ko kuma idan ka bawa mutum bashi, ya yi jinkirin biya, ka ninninka masa kudin da ka ba shi, irin ribar da ake amsa a banki, za ta shiga cikin wannan bangaren.

2. Ribar fi-fiko, kamar yanzu, ki bada naira 1100 tsofafi, a ba ki naira 1000 sababbi, ko kuma ki bayar da shinkafa 'yar gwamnati kwano uku, a ba ki shinkafa ta gida kwano hudu.

 

Duka wadannan nau'oin guda biyu Allah ya haramta su, kuma ya kwashe musu albarka.

Amma idan mutum ya sayi abu naira 5, ya sayar naira 8, wannan ba'a kiran shi riba a musulunci, saboda yana daga cikin riibar da Allah ya halatta, saidai ana so mutum ya saukaka idan yana siyar da kaya, Annabi s.aw. yana cewa : "Rahamar Allah ta tabbata ga mutumin da idan zai siyar da kaya yake rangwame.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr Jamilu Zarewa

24/4/2013

56. TAMABAYA

ZAN AURI MA'AIKACIN BANKI, AMMA INA TSORON CIN HARAM?

Assalamu Alaikum, Dr. Akwai wata kanwata da wani ma'aikacin banki yake so ya aura, ta bangaren mu'amalarsa za mu ce Alhamdulillah, to shi ne take neman menene halarcin auransa a shari'a? Saboda tana tsoron kar ya rika ciyar da ita da dukiyar haramun.  

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 To dan'uwa Annabi  s.a.w.  yana cewa : "Allah ya la'anci mai cin riba da mai rubutata, da wadanda suka yi shaida akan haka" Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 1598.

Hadisin da ya gabata yana nuna haramcin aiki a bankunan da suke mu'amala da riba, saboda ma'aikacin banki zai rubuta ko kuma ya shaida, ko ya taimaka wajan tsayuwar harokokin banki, kamar mai gadi, da dan aike . .

Duba fatawaa Allajanah adda'imah 15\41, da Fataawaa Islamiyya na Ibnu-uthaimin 2\401.

Idan ya zama abin da ma'aikacin banki yake amsa haramun ne, kuma ba shi da wata sana'a sai wannan, akwai hadari a auransa, saboda zai ciyar da matarsa da haramun

 Malamai suna cewa duk mutumin da yake samun kudi ta hanyoyin halal da haram, idan ya maka kyauta za ka iya amsa,  saboda Annabi s.a.w. ya yi mu'amala da yahudawa, kuma a dukiyarsu akwai halal da haram, amma in ba shi da wata sana'a sai ta hanyar haram to ba za ka iya cin dukiyarsa  ba.

Wasu malaman sun halatta aikin banki a bankuna masu kudin ruwa da niyyar kawo gyara, idan niyyar mutum ta tsarkaka. 

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Zarewa

10\4\2015

 

 

57. TAMABAYA

MAHAIFIYATA TA RASU, ANA BIN TA AZUMI, YA YA KAMATA MU YI?

Assalamu alaikum, Malam dan Allah ina da tambaya? tun kafin a kama azumi uwata ba ta da lafiya har akayi sallah, rana ta 16 ga watan karamar sallah  Allah yayi mata rasuwa, shin za mu ranka mata azumi ko ba sai mun ranka ba ? Allah ya saka da hairi.

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 

To malam mutukar rashin lafiyar ta zarce mata, har zuwa lokacin mutuwarta, to ba za ku rama mata ba, tunda ba sakaci ta yi ba, saboda fadin Allah madaukaki  :  "Kuma duk wanda yake mara lafiya ko matafiyi to sai ya rama a kwanaki na daban" Bakara aya ta : 185, wato bayan Ramadahana, idan mara lafiya ya samu sauki, ko matafiyi ya dawo , Ka ga wanda bai samu sauki ba har ya mutu, zai zama bai kai lokacin da zai rama ba, don haka sai ya saraya akan shi.

Amma idan ta samu damar ramawa,  ta yi sakaci ba ta rama ba har ta  mutu, to sai makusancinta ya rama mata, saboda fadin Annabi s.a.w.  : "Duk wanda ya mutu akwai azumi akansa, to sai makusancinsa ya rama masa" . kamar yadda Bukhari ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta: 1851. Duba Fataawa nuru aladdarb lamba ta : 247.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DrJamilu Yusuf Zarewa

1\11\2014

 

 

58. TAMABAYA

YAUSHE NE LOKACIN SALLAR WALAHA?

Assalamu alaikum. Malam daidai wanne lokaci  ne ya da ce a bisa kiyasin lokacin ayi sallar walaha?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

To malam lokacin sallar walaha yana farawa ne daga sanda rana ta daga ta fara zafi, kamar yadda Annabi s.a.w. yake cewa a cikin hadisin Muslim mai lamaba ta : 748 "Sallar walaha lokacin da 'ya'yan rakuma suka fara jin zafi" sannan lokacin yana karewa dab da zawalin rana, da minti sha biyar ko kusa da haka.

 

Allah ne mafi sani.

25/2/2014

Dr. Jamil Zarewa

 

59. TAMABAYA

Assalamu alaikum, Dr. Allah Ta'ala Ya saka da alheri. Don Allah tambayata ita ce: an ce idan mutum ya rasu mahaifi da mahaifiyarsa suna raye amma bashi da 'ya'ya ko mata, iyayen ne kadai za su gaje shi koda yana da kanne da yayyi.

Idan haka ne, to ya za a raba gadon tsakanin mahaifi da Mahaifiyar shi?.

 

Amsa:

Wa alaikumus Salaam wa rahmatullahi wa barakaatuhu, na gode da addu'a.

Dangane da rabon gado tsakanin iyaye kuwa, za a raba abun da ya bari gida uku (3), mahaifi zai dauki kaso biyu (2), Mahaifiya kuma ta dauki kaso daya (1).

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

03/05/2017.

 

60. TAMABAYA

WANDA YAKE GIDA, ZAI IYA HADA SALLOLI SABODA RUWAN SAMA?

 Assalamu alaikum Allah ya karawa

malam ilimi da fahimta. Shin da Allah malam ko mutum zai iya hada sallah shi kadai idan ana ruwa bashi da ikon zuwa masallaci?. Nagode malam.

Amsa

Wa alaikum assalam. To dan’uwa malamai sun yi sabani akan wannan mas’alar zuwa maganganu guda biyu :

 

I. Ya halatta ga wanda yake a gida ya hada

salloli saboda ruwan sama, tun da ruhusa ce Allah ya bawa mutane, don haka ta shafi kowa

da kowa, wannan ita ce maganar Hanabila

kamar yadda Mardawy ya ambata a INSAAF

2\340.

 

2 Bai halatta ga wanda bai je sallar

jam’i ba ya hada salloli saboda ruwan sama,

saboda an yi sauki ne ga wadanda za su je

masallaci don kar su jika jikinsu da ruwa,

wannan wahalar kuma babu ita ga wanda ya yi sallah a gida, don haka rahusar baza ta sameshi ba, sannan kuma shari’a ta yi nufin ta kiyaye sallar jam’i shi ya sa ta saukaka wajan hada

salloli a ruwan sama,don kar mutane su watse sallar jam’i ta tozarta, wannan ita ce maganar

Imamu shafi’i a littafinsa Al’umm 1\195, Afahimtata maganar karshe ta fi inganci, don haka wanda yake gida ba zai hada salloli ba.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR JAMILU YUSUF ZAREWA

12/11/2015


No comments: