GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Sunday 4 September 2022

TAMBAYA TA DARI UKU DA ASHRIN DA DAYA (321) ZUWA TA DARI UKU DA ARBA'IN (340)

321. TAMBAYA

MAI TAKABA ZATA IYA FITA SALLAR IDI?

 

Assalamu alaikum warahmatullah, Barka da war haka. Don Allah YA halatta me takaba ta je sallar Eid?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Bai  halatta ga mai takaba ba ta  fita zuwa Idi, saboda Hadisin  Ibnu Majah Mai lamba ta: (2031)  inda Annabi SAW yake cewa da  Furaia lokacin da mijinta ya Rasu: (Ki zauna a cikin  gidan da  kika samu labarin mutuwar mijinki har zuwa Ki kammala iddarki"

Hadisin da ya gabata yana nuna cewa: Mai takaba

Sunday 24 July 2022

TAMBAYA TA DARI UKU DA DAYA (301) ZUWA TA DARI UKU DA ASHIRIN (320)

 301. TAMBAYA


 AZUMI NAWA AKE YI A WATAN MUHARRAM?


Assalamu Alaikum Malam Don Allah malam azumi nawa akeyi a wannan watan ?


Amsa

Wa Alaikum Assalam To 'yar'uwa ana so mutum ya zage dantse wajan yin Azumi a wannan watan, saboda fadin Annabi (SAW) : "Mafificin Azumi bayan Ramadhana shi ne Azumi  a watan Muharram" kamar yadda Muslim ya rawaito.

Amma Wanda ya fi muhimmanci shi ne na ranar goma ga wata, sai kuma na ranar tara, Annabi S.A.W yana cewa: "Azumin ranar goma ga wata yana kankakare zunubin shekara daya" kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (1162), sannan yana cewa: "Idan na rayu zuwa badi zan azumci ranar ranar tara ga MUHARRAM".

 Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA


31/08/2019.



302. TAMBAYA

TSARAICIN MACE GA 'YAR'UWARTA MACE ?

 

Assalamu alaikum malam Mace taba da jikinta ga mata yan'uwanta don ayi mata wanka saboda kwalliya ko irin dilka da halawa din nan wai haramunne? Ko da ta rufe mamanta da mazaunanta? In haramunne kenan daga ina zuwa ina ne tsiraicin mace da bai kamata yar'uwarta mace ta gani ba? Jazakallahu khairaljazaaa.

 

Amsa :

Wa alaikum assalam

To 'yar'uwa malamai sun yi sabani game

Saturday 23 July 2022

TAMBAYA TA DARI BIYU DA TAMANIN DA DAYA (281) ZUWA TA DARI UKU (300)

 

281. TAMBAYA

WANDA YA SAKI MATARSA A ZUCI BA TA SAKU  BA!

Assalamu Alaikum,

Don Allah Malam, idan mutum da dare ya qudurta zai saki matarsa zuwa safe, amma bai furta ba zuwa safiyar kuma sai ya canza shawara. Shin yaya matsayin auren yake?

Allah Ya taimaka.

AMSA:

Wa alaikumus assalam, Mutukar bai furta ba kuma bai rubuta ba to Ba ta saku ba, saboda Allah ba Ya kama Al'ummar Annabi Muhammad S. A. W.  da zancen zuci kamar yadda hadisi ingantacce ya tabbatar.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

01/08/2017.

 

282. TAMBAYA

WANDA YA MUTU YANA SHAN TABA SIGARI, BAI TUBA BA?

 

Assalamu Alaykum, Ina fatan Dr yana Lafiya. Dan Allah mene ne Hukuncin Mai shan taba (sigari), har ya

Monday 23 December 2013

TAMBAYA TA DARI BIYU DA SITTIN DA DAYA (261) ZUWA TA DARI BIYU DA TAMANIN (280)

261. TAMBAYA

INA YAWAN FITAR DA MANIYYI, SABODA Mijina  BA LAFIYA?

 

Assalamu Alaikum, Dr macece mijinta

ba yada lafiyan aure tsawon lokachi, sai ya

zamana tana yawan releasing ba sai tayi wani

dogon tunani na sha’awaba, ya matsayin

ibadarta yake ?

Amsa

Wa'alaikumus salam.

To gaskiya abin da yake dai-dai shi ne :

 ya nemi magani, in kuma bai samu ba, ana iya raba auran, tun da yana daga cikin manufofin aure, kadange ma’aurata daga fadawa haramun, kamar yadda shararren hadisinnan ya tabbatar. Yawan fitar maniyyi zai iya zama lalurar da za ta iya haifar da saukin sharia, saidai na ki ba zai zama lalura ba, saboda iyayenki za su iya wajabtawa mijin neman magani, in kuma bai samu ba, za ku iya rabuwa, Allah ya azurta kowa dağa falalarsa.

Cigaba da zamanku a wannan halin yana iya jefa

ki cikin hadari, mata nawa ne suka zama mazinata ta hanyar wannan sababin ? ya wajaba ki yi wanka duk sanda maniyyin ya fita, tun da ya fita ne ta hanyar jin dadi.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

262. TAMBAYA

INA YAWAN FITAR DA MANIYYI, SABODA Mijina  BA LAFIYA?

 

Assalamu Alaikum, Dr macece mijinta ba yada lafiyan aure tsawon lokachi, sai ya zamana tana

Sunday 20 May 2012

TAMBAYA TA DARI BIYU DA ARBA'IN DA DAYA (241) ZUWA TA DARI BIYU DA SITTIN (260)

241. TAMBAYA

YAUSHE AKE FITA DAGA I'ITIKAFI

 

Assalamu Alaikum. Malam inaso a fada min mafi rinjayan zance game da lokacin fita daga I'itikafi?

Amsa

Wa'alaikumus salam,

To dan'uwa malamai suna da ra'ayoyi biyu akan wannan mas'alar :

1. Fita  daga I'iitikafi daga zarar an ga watan Ramadhna,  wato bayan rana ta fadi a daren  Idi, saboda  I'itikafi ana  yinsa ne a Ramadhana kuma idan  an ga wata Ramadhana ya  kare.

2. Mai I'itikafi zai iya zama har zuwa lokacin sallar Idi, ta yadda zai fita bayan kammala sallar, Imamu  Asshafi'i yana cewa: "Duk wanda ya yi niyyar koyi da Annabi S.A.W. to  ya  fita daga I'itikafi bayan rana ta fadi in an ga wata, watan ya yi nusan ko ya cika, amma in ya zauna zuwa sallar idi, hakan shi ne yafi"  Imamu Malik yana cewa: "Na samu labarin wasu daga cikin mutanan kirki suna fita daga I'itikafi bayan sallar idi"

Zance mafi inganci shi  ne fita daga I'itikafi bayan ranar daren idi ta fadi, saboda Annabi S. A. W. yana I'itikafin dararen goman karshe ne, su kuma suna fita idan daren IDI ya shiga.

Don neman karin bayani duba Al-majmu'u na Nawawy 6/323 da kuma FaTaawa Allajnah Adda'imah 15/411

Allah ne mafi  sani

24/06/2017

Dr. Jamilu Zarewa

 

Daga *ZAUREN FIQHUS SUNNAH*

242. TAMBAYA

YA SAKI MATARSA A RUBUCE TA SAKU!

 

 Assalamu alaikum malam don Allah yaya wannan yake? Miji ne yayi Sakin da ba a furta ba kawai ya rubuta ne shin tasa ku?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Ta  saku mana,  saboda rubutu

Saturday 19 May 2012

TAMBAYA TA DARI BIYU DA ASHIRIN DA DAYA (221) ZUWA TA DARI BIYU DA ARBA'IN (240)

221. TAMBAYA

SHIN ME NENE ZIHARI?

 

Assalamu alaykum Warahmatullahi wabarakatuh. Don Allah Mallam menene ZIHARI? Allah yaqara ilimi mai amfani.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Zihari shi ne mutum ya kamanta matan shi da wata wanda take muharrama a gare Shi kamar Mahaifiyan sa, kanwar shi ko 'Yar shi da ya haifa.

Wallahu A'alam

Malam Umar Shehu Zaria

03/03/2017

 

 

222. TAMBAYA

ALAMOMIN KARBAR TUBA

 

Assalamu alaikum dan Allah malam akwai hanyar da mutum yake gane Allah ya yafe masa zunubin da yayi, ya kuma nemi yafiya?

 

Amsa

 

Wa alaikum assalam.To dan'uwa

Friday 18 May 2012

TAMBAYA TA DARI BIYU DA DAYA (201) ZUWA TA DARI BIYU DA ASHIRIN (220)

201. TAMBAYA

HUKUNCIN YIN KIRAN SALLAH BA TARE DA TSARKI BA!

 

Assalamu Alaikum, malam ko ya halatta mutumin da yake da janaba ya kira sallah?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa wasu daga cikin malamai suna cewa tsarki ba sharadi ba ne yayin kiran sallah, saboda babu wani nassi ingantacce wanda ya nuna hakan,