GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Friday 18 May 2012

TAMBAYA TA DARI BIYU DA DAYA (201) ZUWA TA DARI BIYU DA ASHIRIN (220)

201. TAMBAYA

HUKUNCIN YIN KIRAN SALLAH BA TARE DA TSARKI BA!

 

Assalamu Alaikum, malam ko ya halatta mutumin da yake da janaba ya kira sallah?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa wasu daga cikin malamai suna cewa tsarki ba sharadi ba ne yayin kiran sallah, saboda babu wani nassi ingantacce wanda ya nuna hakan,

don haka ya halatta ga mai janaba, da mai karamin kari su yi kiran sallah, saidai abin da ya fi shi ne yin cikakken tsarki kafin kiran sallah, saboda fadin Annabi s.a.w " Ina kin na ambaci Allah alhali ba ni da tsarki", kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai lamba ta :16, kuma Albani ya inganta shi a Sahihu-sunani Abi-dawud 1\16.

Don neman Karin bayani duba : Fathul-bary 3\113 da Majmu'u fataawaa wa makaalatin mutanawwi'a 10\338.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Zarewa

27/6/2015.

 

 

202. TAMBAYA

INA YAWAN WAYA DA BURDURWATA, KO YA HALATTA A SHARI'ANCE?

 

Assalamu alaikum malam Dan Allah ina tambaya. Namiji ne yakeso ya qara aure to shine bayan ya dawo gida da dare sai budurwar ta riqa kiran shi ko kuma ta riqa turo txt, shikuma idan matarshi tana kusa sai ya riqa avoiding amma data dan daga sai shima ya fara respindingو ko ya kira ta kuma idan asuba tayi sai ta kirashi. To shine matar ba taso, dan Allah a Shari'ance yanada laifi ko ba shi da ? sannan matar zata iya neman ya dena ko kuwa ta shiga rayuwarsa ne a shari'ance ?

Amsa

Wa alaikum assalam To dan'uwa yana da kyau ka san cewa matar da kake nema aure ba muharramarka ba ce, don haka bai halatta ka dinga hira da ita ba, sai gwargwadon bukata.

Yawan hira da budurwa da jin dadin zancenta, yana daga cikin abubuwan da suke kaiwa zuwa ga fitina, mai AHLARI ya kirga jin dadin zancen wacce ba muharrama ba daga cikin ayyukan da Allah ya hana.

Duk wanda yake yawan hira da matar da ba muharramarsa ba, yana jin dadin zancenta, Allah zai iya haramta masa jin dadin zancen matarsa ta halal.

Ya wajaba hirarka da buduwarka ta zama gwargwadon bukata, saboda jin dadin zancenta, zai iya kai ku ku aikata katon sabo, yana daga cikin ka'idojin shari'a toshe duk hanyar da take kaiwa zuwa barna.

Zunubi shi ne abin da ya sosu a ranka kuma ka ji tsoron kar mutane su yi tsinkayo, kamar yadda hakan ya tabbata a hadisin Muslim mai lamba ta: 2553.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

4\1\2016.

 

203. TAMBAYA

MAGANIN QARFIN MAZA?

 

Assalamu alaikum, Malam mutum ne yana da chemist yana sayar da magunguna. Ya halatta ya sayar da maganin qarfin maza ga wanda yake so ya biya bukatar iyalinsa? Allah ya qarawa Dr. Jameel imani da lafiya da ilimi, gaskiya muna amfana

Amsa

Wa alaikum assalam, In har an jarraba an samu yana amfani kuma likitoci sun tabbatar ba ya cutarwa ya halatta a siyar da shi don aure ya gyaru, a kara samun donkon soyayya, saboda saduwa tsakanin ma'aurata turke ne tsayayye, wanda in ya goce aure ba zai tafi saiti ba, yana daga cikin ka'idojin Sharia duk harkokin mutane na yau da kullum wadanda ba ibada ba ne sun halatta, in har ba'a samu nassin da ya hana ba.

Addinin musuluci ya haramta duk abin da yake cutarwa, kamar yadda nassoshi masu dinbin yawa suka tabbatar, wannan yasa duk maganin da likitanci ya tabbatar cutarsa ta fi amfaninsa yawa ya wajaba a guje shi, Tunkude cuta ginshike ne a cikin addinin musulunci.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

23/05/2016

 

204. TAMBAYA

MATATA TA YI BARI, AMMA JINI YANA DAUKEWA YA DAWO

 

Assalamu alaikum, Malam ga wata tambaya a taimakama ,matata ta samu bari to abun bai gama fita ba tana zubar da jini sai ya dauke kwana hudu sai ya dawo sai ta fara sallah sai ya dawo yanzu kusan wata biyu kenan, shin za ta ci gaba da sallah tunda ya zama kamar jinin ciwo?.

Amsa:

Wa'alaikumus Salaam. Idan mace ta yi barin ciki, to babban abin da za ta lura da shi, shi ne abin da ta yi barin, idan halittar Mutum ta bayyana ga abin da ta yi barin ta yadda za a iya ganin hannu ko kafa da makamancin hakan, to wannan jinin ya zama jinin biki. Don haka sai ta bar Sallah, Azumi, Saduwa da Miji da sauran dukkan abin da aka hana mai biki aikatawa.

Amma idan abin da ta yi bari yana nan a matsayin maniyyi ko gudan jini ko tsokar da babu halittar Mutum a jikinta, to wannan jinin ba jinin biki ba ne, jinin ciwo ne, don haka za ta yi Sallah, Azumi, da sauran duk abin da aka halatta ma mace mai tsarki sai dai duk lokacin da za ta yi sallah, to sai ta yi tsarki ta sake yin Alwala.

Kuma hukuncin jini yana tabbata ne tun daga lokacin da jinin ya fara fitowa koda bata kammala zubar cikin ko haihuwar ba, domin Malaman Musulunci sun hadu akan cewa mace tana iya fara zubar da jinin biki kafin haihuwa indai ta fara nakuda, sai dai Ibn Hazam shi ne yace jinin biki ba zai fara zuwa ba sai mace ta haife dukkan abin da ke cikin cikinta, amma dai tabbatacciyar magana shine: jinin biki yana fara zuba ne a lokacin da Uwa (wadda take fadowa bayan haihuwa a hade da cibin jaririn) ta ballo daga bangon mahaifa.

Allah ya bamu ikon ganewa da gyarawa.

Amsawa

Malam Ibrahim Jushi

16/05/2017.

 

205. TAMBAYA

DALIBIN DA YA YI AURE DA NIYYAR ŞAKI, IN YA GAMA KARATUNSA?

 

Assalamu alaikum. Malam shin ya halasta mutum yaje karatu wani kasan da Ba nasaba zaiyi shekara 5 sai yayi aure da niyan idan ya gama makarantan nashi sai ya saketa ya koma gida?

 Amsa

Wa'alaikum assalam, wasu malaman sun halatta hakan, sai dai zance mafi inganci shi ne rashin halarcinsa, saboda ya yi kama da auran mutu'a, sannan kuma hakan ya sabawa wasu daga cikin manufofin aure. 

Kamar dawwamammar soyayya da kuma debe kewa, Aya ta 21 a suratu Arrum ta tabbatar da cewa: an shar'anta aure ne dön ka nutsu da matar da zaka aura,  wannan manufar ta goce a aure da niyyar saki.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

12/05/2016

 

206. TAMBAYA

Malam ina neman shawara

 

Malam ina neman shawara inada saurayi me ilimin addini dana buko amma mamana tana sona aure wani mutum mara ilimi kuma ni bana sansa toh malam wazan zaba aciki?

ASSALAMU ALAIKHUM

Amsa

Wa'alaiku mussalam, Hadisi ya tabbata wani mutum yazo wajan Annbi S.A.W yace dashi: cikin mutanan duniyannan wanene ya kamta nayi mishi biyayya sai Annabi S.A.W yace dashi: mahaifiyarka ya sake cewa sannan wa? Annabi S.A.W yasake cewa dashi mahaifiyarka, yasake cewa sannan wa? Annabi S.A.W yasake cewa dashi mahaifiyarka, ya sake cewa sannan wa Annabi S.A.W yace mahaifinka.

Muhimmancin hakkin uwa bayan hakkin Allah S.A.W da na Annabi S.A.W babu wanda yafi shi girma daga ita sannan mahaifi, dan haka wajibine bin mahaifiya.

                            SHAWARA

Ki lallabata har ta gamsu kiyi kokari ta wajan yi mata biyayya da kuma bin kawayanta da yan uwanta cikin ladabi wajan su saka baki dan shawo kanta har Allah yasa ta gamsu ta baki wanda kike so.

Muna Addu'a Allah ya zaba miki wanda yafi Alkhairi.

Rubutawa:- Abubakar Eka.

 

207. TAMBAYA

ZAN IYA DAUKAN AZUMIN NAFILA A JAJIBARIN RAMADAN?

 

 Assalamu alaikum

Menene hukuncin wanda keyin azumin litinin da alhamis sai  azumin Ramadan ya kama ranan juma'ah  to ya halasta yayi azumin  ranan  alhamis din Alhalin washe Gari azumin Ramadan?

Amsa

Wa alaikum assalam,

In ya saba yi babu laifi ya azumta, saboda hadisin da Annabi S.A.W. yake cewa: " Kada ku gabaci Ramdhana da azumin yini daya ko biyu sai Fa in azumin da mutum ya saba yi ne, kamar yadda Bukhari ya rawaito hakan a hadisi mai lamba ta: 1914 da kuma Muslim a hadisi mai lamba: 1082.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

17/05 /2017

 

208. TAMBAYA

ZAN IYA AURAN 'YAR KANWAR MATATA?

 

Assalamu alaikum Malam, Ya halatta mutum ya auri yar qanwar matarsa?

Amsa

Wa alaikum assalam, ya halatta ya aure ta, bayan ya saki matarsa, amma bai halatta ya hada su ba saboda innarta ce, Annabi S.A.W yana cewa: "Ba'a a hada mace da goggonta, ba'a hada mace da innarta a auratayya, saboda in kuka yi haka, za ku lallata zumunci ku" kamar ayadda ibnu Hibban ya rawaito.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

20\5\2016

 

208. TAMBAYA

SANYA ZOBEN AZURFA A DAN YATSAN DAMA?

 

Assalamu Alaikum Malam ga wata tambaya nan kamar haka:Assalam da fatan kana lpy! pls ga tambayana menene hukuncin sa AZURFA ZOBE a hanun dama shin akwai wata illa ne koh kuma manzon Allah baisaba???

Amsa

 Walaikum assalam.To dan'uwa ya halatta a sanya zoben azurfa a karamin dan yatsan hagu da kuma dama, Nawawy ya hakaito Ijma'in kasancewar hakan Sunna, saidai akwai hadisi mai lamba ta :2078 a Sahihi Muslim wanda yake nuna haramcin sanya zobe a dan yatsan tsakiya da wacce take binta, wasu malaman kuma sun dauki hanin a matsayin karhanci ba haramun ba.

Don neman karin bayani duba Al-majmu'u na Nawawey 4\340.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

28\12\2015

 

209. TAMBAYA

DAN ZINA ZAI GAJI MAHAIFIYARSA?

 

Assalamu alaykum. Malam don Allah Malam in nada tanbaya, Malam mace ce tayi ciki  batare da aure ba, ta haihu kuma tana da kudi sai Allah ya mata rasuwa toh malam yaron zai ci gadonta ?.

Amsa

Wa alaikum assalam,

idan mace ta yi cikin shege kuma ta haifi Da, daga baya ta mutu Dan zinar da ta haifa zai gaje ta, saboda Allah madaukakin sarki a cikin suratun Nisa'i aya ta : 10 ya yi wasiyya a bawa 'ya'yaye gado, Dan zina kuma yana cikin jerin 'ya'yayen mahaifiyarsa, wannan yasa zai gaje ta.

Dan zina ba ya gadon mahaifinsa a wajan mafi yawancin malamai, ko da kuwa ya yarda dansa ne.

 Allah ne mafi sani

Don neman karin bayani duba : Sunanu Attirmizy hadisi mai lamba ta: 2113 da kuma Tabyinul haka'ik 6\214.

Dr. Jamilu Zarewa

25\5\2016

210. TAMBAYA

HUKUNCIN AUREN HANNU (Masturbation)?

 

Assalmu alaikum, Allah ya kara ma malam lapiya da imani, malam dan Allah menene hukumci masturbation (Istimna'i) a musulunci.

Amsa

Wa alaikum assalam,

To 'yar'uwa  Babu nassi ingantacce bayyananne yankakke da yake haramta wasa da al'aura har maniyyi ya fito, duk hadisan da suka zo ba su inganta ba.

Saidai wasu malaman sun haramta auran hannu saboda aya ta 6 a Suratul Muminun ta iyakance biyan bukatar sha'awa ta hanyar matar aure ko bayi kawai, wannan sai ya nuna abin da ba wadannan ba ba'a iya biyan bukata ta hanyar su.

 Yin wasa da al'aura har maniyyi ya fita yana haddasa matsaloli a likitance, saidai yana daga cikin ka'idojin shari'a ; idan cututtuka biyu suka hadu ya zama babu yadda za'a yi sai an aikata daya daga ciki sai a zabi karama a aikata, wannan yasa Imamu Ahmad da Ibnu Hazm suka  halatta auran hannu ga wanda ya ji tsoron zina kuma ba shi da halin da zai yi aure.

Idan mu ka ce auran hannu haramun ne, saidai barnar dake cikin zina tafi girma, domin zina akwai keta alfarma a ciki, sannan tana kaiwa ga cakuduwar nasaba, ta yadda za'a haifi 'ya'ya gantalallu, marasa asali, wannan ya sa magana ta biyu ita ce mafi inganci, mutukar an samu sharudan da suka gabata.

Don  neman Karin bayani duba : Muhallah 12\407 da Majmu'ul fataawaa 34\146>

Allah ne mafi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

23\1\2016

 

211. TAMBAYA

SHIN AKWAI ZAKKA A CIKIN ALBASHI?

 

Assalamu alaikum.Malam yaya zakkar ma'aikaci ya kamata ta zamo? Domin wasu ma'aikatu sukan bada alawus a dunkule wanda ya isa zakkah to amma wasu sukanyi gini ko sayen filaye ko gonaki da kudin kafin shekara ta zagayo sun kare. 

Amsa

Wa alàikum assalam.To dan'uwa, hukuncin wannan albashi zai fara ne daga lokacin da ya shiga mulkinsa, don haka mutukar ba su shekara ba, to babu zakka a ciki, domin ba kawai samun nisabi ne ya ke wajabta zakka ba, dole sai an samu zagayowar shekara daga lokacin da kudin su ka shiga mulkinsa, don haka duk albashin da ya kai zakka, kuma aka ajjiye shi ya shekara to ya wajaba a fitar masa da zakka, amma mutukar shekara ba ta zagayo masa ba, to zakka ba ta wajaba ba akan wanda ya mallake shi.

Saidai yana daga cikin dabarun da sharia ta haramta, mutum ya yi abin da zai sarayar masa da wajibi da gangan, don haka mutukar ya sayi filayan ne da nufin kaucewa fitar da zakka, to tabbas ya sabawa Allah.

Allah ne ma fi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

14/5/2014

 

212. TAMBAYA

HUKUNCIN DILLANCI DA HOTUNAN 'YAMMATA

 

Assalamu alaikum. Malam menene hukuncin 'yan matan da suke bada hotunansu ga tsofafi don su nema musu mijin aure?

AMSA

Wa alaikum assalam Addinin musulunci ya haramta kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, amma ya halatta ka kalli mace, idan kana so ka aure ta, kamar yadda ya zo a cikin hadisi, inda Annabi s.a.w. yake cewa : "Idan dayanku yana neman aure, to in ya sami damar kallon abin da zai kira shi zuwa aurenta, to ya aikata hakan" ABU DAWUD

Malamai sun yi sabani akan wurin da ya kamata mutum ya kalla a jikin mace lokacin da ya je neman aure :

1. Akwai wadanda suka ce zai kalli fuska da tafin hannu ne kawai.

2. Wasu malaman sun tafi akan cewa : zai kalleta a kayan da take sawa a cikin gida, ta fuskace shi ya kalle ta, sannan ta juya baya ya kalleta.

Wannan ra'ayin shi ne ya fi dacewa, saboda ta haka mutum zai san yanayin matar da zai aura.

Ta hanyar bayanan da suka gabata, za mu iya fahimtar cewa aikin dalilin aure ya hallata, amma da sharuda, ga wasu daga ciki :

1. Ya zama hoton ya fito da asalin fuskar matar, bai KWARZANTA ta ba, ta yadda za'a iya yaudarar namijin, ko a rude shi.

2. Ya zama wacce za'a bawa hoton mai amana ce, ta yadda ba za ta nunawa wanda ba shi da nufin aure ba, saboda asali ya haramta ayi kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, sai ga wanda yake nufin aurarta, wannnan yana nuna cewa, bai halatta asa irin wannan hoton na neman aure ba , a face book, ko a jarida.

3. Ka da hoton ya kun shi fito da tsaraici, ya wajaba a tsaya a iya inda shari'a ta bada umarni.

4. Zai fi dacewa ace mace ce za ta yi dalilin aure, saboda in namiji ne, zai iya fitinuwa da hotunan da yake gani, sai barna ta auku, don haka ita ma macen ya wajaba ta ji tsoron Allah a cikin aikinta.

Allah shi ne ma fi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

26/5/2014

 

213. TAMBAYA

KO ZAN IYA BAWA KANNENA ZAKKA?

 

Assalamu alaikum,

Malam ansha ruwa lafiya? Malam ko ya halatta imba ma'aikatana  zakka?da kannena?.

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Wa alaikum assalam. To dan'uwa ba ya halatta musulmi ya bada zakka ga wadanda wajibi ne akansa ya ciyar da su; kamar iyaye maza da mata, kakanni; maza da mata, da kuma 'ya'ya da 'ya'yan 'ya'ya ; saboda bada zakka ga wadannan zai sauke masa nauyin ciyar da su da ya ke wajibi akansa; daga nan kuma sai amfanin bada zakkar ta dawo kansa.

Amma kanne kuwa, to ciyar da su bai wajaba akanka ba, don haka ya halatta ka ba su zakka, haka nan ma'aikatanka.

Sannan daga cikin ka'idojin da malamai suke fada a wannan babin shi ne duk mutumin da idan ka mutu ba zai gaje ka ba, to ya halatta ka ba shi zakka, ka ga  kuwa kanne, ba sa gado mutukar akwai 'ya'ya.

Duba fiqhul-muyassar shafi na : 145

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

08/07/2014

 

214. TAMBAYA

MUNA JINKIRTA WANKAN JANABA ZUWA BAYAN ASUBA, A WATAN RAMADANA?

 

Assalmu alaikum, malam ina da tambaya shin meye

hukuncin matan da za su sadu da mijinsu lokacin azumi,

amma ba za su yi wanka ba har sai alfijir ya fito, shin yaya

matsayin azumin su yake.? Nagode

Amsa

Wa alaikum assalam, ya halatta mace ta sadu da mijinta su

jinkirta wanka zuwa bayan ketowar alfijir a watan

Ramadhana, a zuminsu kuma ya inganta, saboda Annabi

S.a.w yakan yi haka da matansa, kamar yadda iyalansa

A'isha da Ummu Salama suka rawaito hakan, kuma Muslim

ya fitar da riwayar a Sahihinsa a hadisi mai lamba ta: 1874.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

21/05/2016

 

215. TAMBAYA

BANA SO NA SHA AZUMI, KO ZAN IYA SHAN MAGANIN HANA HAILA?

 

Assalamu alaikum,

Allah ya gafarta malam, azumi ya zo ni kuma ba na son na sha ko azumi daya, to shi ne na sayi maganin da zai hanani yin al'ada na sha, bayan mun hadu da kawata, sai take ce min wai babu kyau, shi ne na ce mata ban yarda ba, zan tambayi malamai, don Allah malam a kara min haske?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa amfani da maganin da yake hana haila ya halatta, Idan ya zama ba zai cutar ba, amma idan zai cutar, to ya haramta saboda fadin Allah “kar ku jefa kawunanku a cikin halaka” suratu Albakarah aya ta 1952. Saidai duk da cewa hakan ya halatta da sharudan da suka gabata, amma barinsa shi ya fi, sai idan bukatar hakan ta taso, saboda mutum ya zauna akan yadda yake ya fi masa kwanciyar hankali akan ya yi abin da zai canza dabi’arsa, musamman ma wasu daga cikin kwayoyin na zamani suna dagula kwanakin haila, kamar yadda ya bayyana gare mu, sai a kiyaye.Don neman karin bayani, duba : Dima'uddabi'iyya shafi na : 54 .

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

22\6\2015

 

216. TAMBAYA

SHIN AMAI NA KARYA AZUMI?

 

Assalamu alaykum'm Malam Dan Allah inada tambaya,nice ina azumi se nayi irin Dan aman nan wanda ake ce masa aman kaji,Dan kadanne ba wae amai da yawaba,to malam ya matsayin azumi na naji ance amai yana karya azumi.Allah y qarawa malam Lpy.

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Duk aman da akayi kadan ko mai yawa ba da gangan ba toh baya karya azumi amma idan an kakaro shi ne to azumi ya karye, Don fadar manzon Allah cikin hadisin Abu huraira wanda ke cikin sunan na imam tirmizi 720.

Don haka dai babu sabani tsakanin malamai cewa duk wanda amai ya rinjaye shi toh azumin sa na nan amma wanda ya kago amai da kansa to azumin sa ya baci, aduba:

Al'Mugni 4/368

Wallahu A'alam

Malam Nuruddeen Muhammad (Mujaheed)

29/05/2017

 

217. TAMBAYA

SUFRA DA KUDRA DA HUKUNCINSU

 

Assalamu alaikum,

Dan Allah Malam Ina bukatar bayani akan "KUDRA da kuma SUFRAH", Allah ya saka da Alkhairi.

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa, Wannan yana daga cikin mas'aloli masu mutukar muhimanci, amma ga abin da ya sawwka game da haka :

Sufra na nufin mace ta ga ruwa mai fatsi-fatsi kamar ruwan ciwo, ya fito daga gabanta.

Kudra kuwa na nufin : ruwa ya ringa fitowa daga farjin mace, wanda kalarsa ta ke kasancewa tsakanin fatsi-fatsi da baki wato kamar ruwa gurbatacce,

Dangane da hukuncinsu kuwa : idan daya daga cikinsu ya kasance a tsakiyar haila ne ko kuma yana hade da haila kafin ta sami tsarki to wannan ana saka shi a cikin haila, idan kuma bayan tsarki ne to ba haila ba ne saboda fadin Ummu adiyya mun kasance ba ma kirga sufra da kudra bayan tsarki a cikin haila) Abudawud ya rawaito shi da sanadi mai inganci,

A hadisin A’isha kuma (Mata suna aiko mata da abin da suke sawa lokacin da suke haila a jikinsa akwai sufra (wato ruwan da yake kama da ruwan ciwo) sai ta ce musu kada ku yi gaggawa har sai kun ga farin ruwa ya fito, ta yadda za mu yi amfani da hadisin Ummu adiyya bayan an sami tsarki, ma’ana ko ta ga sufra da kudra ba za ta kirga su a cikin haila ba, hadisin A’isha kuma za mu yi amfani da shi idan tana cikin haila ta yadda za ta kirga da su.

ALLAH ne mafi sani.

5/12/2014

Dr. Jamilu Zarewa

 

218. TAMBAYA

YA YI WA MATARSA ZIHARI SAI YA SAKE TA KAFIN YA YI KAFFARA?

 

Assalamu Alaikum, Malam ina da tambaya? Namiji ne ya yi wa matarsa zihari, maimakon ya yi kaffara sai ya sake ta, ya sake wani auren. Malam ya matsayin wannan sakin da matsayin auren?.

Allah ya bada ikon isar da wannan sako ga  Malam.

Amsa

Wa alaikum assalam, Auransa na biyun ya inganta saboda ba su da alaka da juna.

Wasu Malaman sun tafi akan cewa mutukar saki uku ne, to wancan ziharin ya warware, amma in saki daya ne kuma ya yi kome, to bai halatta ya taba ta har sai ya yi kaffarar ziharin, kamar yadda Ibnu Khudaamah ya fada a cikin Al-Mugni.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

01/06/2017.

 

219. TAMBAYA

TANA AZUMI SAI MIJINTA YA SUMBACETA?

 

Malam macece tayi kitso alhalin tana azumi sai mijinta yaga kitson ya basa sha'awa saiya sumbacesa ita kuma take sha'awa tazo mata harta jika pant dinta

Amsa

Wa akaikumus salamTo yar uwa da farko dai anyi wasa da azumi kwarai da gaske kuma ba daidai bane kina azumi ki bari mijinki ya sumbaceki ta yadda har zaki fitar da wani abu dazai bata miki azumi' wannan akwai ganganci a ciki.

Amma shi azumin nafila dama mai shi yanada yan'cin ya karyashi koya cigaba Annabi S.A.W ya fada cikin hadisi sahihi mai azumin nafila shine sarkin kansa idan yaga dama ya karya manzon Allah s.a.w. ya bada wannan damar.

Malamai suna cewa fitar maziyyi idan har maziyyine ya fita karamar sha'awa kenan zance mafi inganci baya karya azumi amma idan maniyyi ne ya fita to azumi ya karye shikenan idan na nafila ne bakida lada idan kuma farilla ne akwai kaffara akansu bisa kaulin malamai amma wasu malaman sukace sai anyi jama'i kaffara take wajabta idan nafilane shikenan idan kuma na farillah ne saiki rama guda daya wannan shine zance mafi inganci.

Allah shine mafi sani.

Amsawa

DR. ABDALLAH GADON KAYA

 

220. TAMBAYA

INA CIKIN SADUWA DA MIJINA A RAMADHANA SAI ALFIJIR YA KETO!​​

 

Assalamu alaikum Malam muna cikin saduwa da mijina a cikin wannan wata, sai muka ji kiran sallar asalatu, me ye hukuncin azuminmu?

Amsa

Wa alàikum To 'yar'uwa mutukar kuna jin kiran sallar, kun maza da sauri, kun datse saduwar da kuke yi, to azumin ku yana nan, amma in har kuka ci gaba, da yi ko da na second daya ne, to azuminku ya karye, kuma za ku yi kaffara ku duka, idan kin yi masa biyayya, in kuma takura miki ya yi, to zai yi kaffara shi kadai.

Duba Almugni: 3\65.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

18/06/2015


No comments: