GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Thursday 17 May 2012

TAMBAYA TA DARI DA TAMANIN DA DAYA (181) ZUWA TA DARI BIYU (200)

181. TAMBAYA

ABUBUWAN DA SUKE KAWO NUTSUWA A CIKIN ZUCIYA

                 

Assalamu alaikum malam Don Allah malam ta yaya zan samu nutsuwa a cikin zuciya ta?, saboda wani lokacin sai na ji zuciyata, kamar an kunna min wuta, wasu lokutan kuma bakin ciki ya hana ni bacci

Amsa

Wa alaikum assalam To dan'uwa akwai

abubuwan da malamai suka yi bayani cewa : suna kawo nutsuwa a zuciya, ga su kamar haka

1.Cikakken tauhidi, ta yadda mutum zai bar duk wata shirka da bidi'a da abin da yake kaiwa zuwa gare su .

2.Shiriya da hasken da Allah yake jefawa a zuciyar bawa, wanda duk lokacin da aka rasa shi, sai bawa ya kasance cikin kunci.

3.Ilimi mai amfani, saboda duk lokacin da ilimin mutum ya yalwata, zai samu jindadi a zuciyarsa.

4.Dawwama akan zikirin Allah, saboda fadin Allah "Wadanda suka yi imani zuciyoyinsu suna nutsuwa da zikirin Allah" Suratu Arra'ad aya ta 28

5. Kyautatawa bayin Allah, saboda duk mutumin da yake yin kyauta zai kasance cikin kwanciyar hankali, kamar yadda marowaci yake kasancewa cikin kunci.

6. Fitar da kyashi da hassada daga zuciya.

7. Barin kallo da zancen da ba shi da fa'ida.

8. Barin baccin da ba shi da amfani.

9. Cin abinci gwargwadon bukata, da rashin karawa akan haka.

10. Rashin cakuduwa da mutane sai gwargwadon bukata.

Kishiyoyin wadannan abubuwa su ne suke jawo bakin ciki da damuwa da kuma kunci.

Don neman karin bayani duba zadul-ma'ad 2\22

Allah ne ma fi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

17/8/2014

 

182. TAMBAYA

MAI TAKABA ZATA IYA FITA SALLAR IDI?

 

Assalamu alaikum warahmatullah, Barka da war haka. Don Allah YA halatta me takaba ta je sallar Eid?

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Bai  halatta ga mai takaba ba ta  fita zuwa Idi, saboda Hadisin  Ibnu Majah Mai lamba ta: (2031)  inda Annabi SAW yake cewa da  Furaia lokacin da mijinta ya Rasu: (Ki zauna a cikin  gidan da  kika samu labarin mutuwar mijinki har zuwa Ki kammala iddarki"

Hadisin da ya gabata yana nuna cewa: Mai takaba ba za ta fita ba sai in akwai lalura, sallar idi kuma ba ta cikin lalorori a sharia.

Imamu  Ashshaukani a cikin Nailul Audaar 3/343 ya yi bayani cewa "Dukkan Mata ana fitar da su daga gidanjansu Don su halarci idi, in ban da wacce take iddar mutuwa.

Allah ne mafi Sani

Dr. Jamilu Zarewa

03/09/2017

 

183. TAMBAYA

NAMIJI ZAI IYA KARA GASHI!

 

Assalamu alaikum

Malam me hukuncin wanda ya qara gashi akansa irin wanda maza suke zuwa ana musu surgery ashuka musu gashin musamman ga masu sanko ko kuma waenda gashin kansu ke cincinyewa wai saboda su zama dai dai da sauran

Amsa

Wa alaikum assalam,

Bai  halatta ga namiji ya kara gashi ba,  saboda hakan canza halittar Allah ne.

Kasancewar Allah ya haramtawa mata kara gashi a cikin hadisai ingantattu duk da cewa suna tasowa NE a cikin kwalliya kamar yadda ayar Suratu Azzukruf ta tabbatar, hakan sai ya nuna namiji ne ya fi cancanta da haramcin, tun da shi ba'a  yi shi don Ado ba.

Malamai suna cewa duka nassoshin da suke haramtawa mata kara gashi, to maza ma suna ciki,  amma an kebance mata ne da haramcin saboda su ne suka fi yawan aikatawa.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

03/09/2017

 

184. TAMBAYA

CIWO YA DAMENI, ZAN IYA AMSAR BASHI DA RUWA DON NA YI MAGANI?

 

Assalamu alaikum, mutum ne yake cikin halin rashin lafiya, kuma al'ummah da suke tare ba masu taimakawa ne ba,gashi wannan ciwon nason ya hallaka shi, shi kuma ba shi da kudi kuma ba shi da hanyar kudi, malam shin zai iya karbar kudin LOAN na govt don surika cirewa duk wata, ko babu halin haka nagode Allah yakara karfin imani da basirah

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Ya halatta ya amshi rancen mai ruwa, mutukar abin da yake damunsa, ya kai wancan halin da ka ambata, saboda larura tana halatta abin da aka hana, saidai ya wajaba ya amsa gwargwadon bukata.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

3\6\2015

 

185. TAMBAYA

NA SHA NONON MATATA, YAYA AURANMU?

 

Assalamu alaikum.Don Allah malam ya matsayin mutumin da ya sha nonon matarsa,  ya aurensu  yake ?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa Allah madaukakin sarki ya halatta maka jin dadi da dukkkan bangarorin jikin matarka, in ban da dubura ko kuma saduwa da ita lokacin da take haila,  don haka  ya halatta ka tsotsi nononta mutukar babu ruwa a ciki, amma idan akwai ruwa a ciki, to malamai sun yi sabani akan halaccin hakan zuwa  maganganu guda biyu :

1. Ya halatta, saboda kasancewar nonon da yake haramta aure shi ne wanda aka sha kafin yaro ya cika shakaru biyu,  saboda fadin Annabi s.a.w. "Shayarwar da take haramtawa, ita ce wacce yaro ya sha saboda yunwa" , Bukhari lamba ta : 5102,  ma'ana lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono, saboda shi ne abincinsa, shi kuma wannan ya faru ne bayan mutum ya girma don haka ba zai yi tasiri ba wajan haramta aure,  wannan ita ce maganar mafi yawan malamai.

2. Bai halatta ya sha ba, saboda ko da yaushe mutum ya sha nonon mace to ta haramta a gare shi, domin Annabi s.a.w. ya umarci matar Abu-huzaifa da ta shayar da Salim,  don ta haramta a gare shi, kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2636, tare da cewa a lokacin Salim ya riga ya girma,  wannan sai yake nuna cewa idan babba ya sha nono to zai yi tasiri wajan haramcin aure.

Zancen da ya fi karfi shi ne ya halatta miji ya sha nonon matarsa, saidai rashin shan shi ne ya fi, saboda fita daga sabanin malamai yana da kyau.

 Don neman Karin bayani duba : Bidayatul-mujtahid 2\67

 Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

1\11\2014

 

 

186. TAMBAYA

NA RABA  GADONA KAFIN NA MUTU, KO YA INGANTA?

 

Assalamu alaikum. malam don Allah ina da tambaya da fatan za'a amsamin, wai mutum zai iya rabawa iyalansa gadansa kafin yamutu wai hakandin ya halatta? nagode

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa malamai suna cewa hakan bai inganta ba, saboda dalilai, ga wasu daga ciki :

1. Hakan yana daga cikin gaggauta abin da Allah ya jinkirta, saboda Allah ya sanya rabon gado ne, bayan mutuwa.

2.  Zai iya yiwuwa daya daga cikin  iyalan nasa ya mutu kafin shi, ka ga sai a samu kwan-gaba kwan-baya.

3. Yana iya jawo hassada saboda daya daga cikin magadan zai iya yin kasuwanci da gadon da aka ba shi ya samu riba mai yawa kafin magajinsa ya mutu, wanda hakan zai iya kawo hassada tsakanin magada, don za su ga da ba'a yi gaggawar rabawa ba da ya kasance daga cikin rabonsu.

4. Yana daga cikin sharudan gado tabbatar da mutuwar  wanda za'a gada .

Allah ne mafi sani 

Dr. Jamilu Zarewa

6\7\2015

 

187. TAMBAYA

SHIN  MUSULMI ZAI IYA AIKI A CHOCHI, DON SAMUN NA KALACI?

 

Assalam alaikum malam ina da tambaya; misali ni brikilane kuma na kasance musulmine sai aka ban contrc din gini na church, ogana ya ce mu za muyi; yaya matsayin mu yake idan munyi wannan aikin?

Amsa:

Wa alaikum assalam To dan'uwa  malamai sun yi bayani cewa : bai halatta musulmi  ya zama Birkila a  Chochi ba, saboda hakan yana daga cikin taimakawa aikata zunubi, kuma zai iya jawowa mutum ya ga yadda ake shirka da Allah, wanda hakan zai  iya masa tasiri.,

Allah madaukaki yana cewa " kada ku yi taimakekeniya wajan aikata  sabo", " suratul Al-maidah aya ta : 2, sannan duk abin da yake kaiwa zuwa barna, to zai zama haramun ko makaruhi.

Don neman kari bayani duba : Al'umm ta Shafi'i    4/213.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

19\5\2015

 

188. TAMBAYA

ZAN IYA HULDA DA MAI KUDIN LUKUDU?

 

Assalama alaikum. Malam dan Allah

Ina aiki ne  akarkashi wani Alhaji Amman a nazargin sa da wai  kudisa bana halal bane wasu suce dan  luwadi ne  wasu  kuma suce kudin lukudu ne ina  so insan  yadace nacigaba damai aiki ko inbari Allah y kara lpy da ilimi da kafin basira ameen

Amsa

Wa alaikum assalam, Ya wajaba ka tabbatar da hakan kafin ka yanke hukunci.

Ba'a gina hukunci a musulunci akan shakka ko zato mara rinjaye, saboda wani sashen zaton zunubi ne kamar yadda aya ta (12) a cikin suratul Hujraat ta tabbatar da hakan.

Idan wani bangare na kasuwacinsa halal ne wani kuma Haram ne za ka iya hulda da shi, saboda Annabi S.a.w. ya yi mu'amala da yahudawa kuma a cikin dukiyarsu akwai halal akwai kuma haram.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

16/09/2017

 

189. TAMBAYA

RAYUWAR DUNIYA A WAJEN MAGABATA NA-KWARAI

 

Aun bn Abdullahi yana cewa : "Wadanda su ka zo gabaninmu sun kasance suna sanya abin da ya ragu na lahirarsu ga duniyarsu, amma sai ga shi ku, kuna sanya abin da ya ragu na duniyarku ga lahirarku"

Yana nufin mutanen zamaninsa ba sa bawa Allah sai dan lokacin da ya dan ragu na harkokin duniyarsu.

Subhanallah in da ya zo a wannan zamanin me zai fada!!!

Wallahi na ga mutumin da kullum yake hada salloli guda biyar a lokaci daya, yakan faro daga azahar din jiya har ya zo asubar yau, gobe ma haka zai yi.

Rubutawa

Dr.Jamilu yusuf Zarewa

may 2014

 

190. TAMBAYA

ABUBUWAN DA SUKE TAIMAKAWA WAJAN SAMUN ILIMIN ADDINI

Assalamu alaikum Akaramukallahu Allah ya kara basira, kuma ina neman shawara cewa ni ina son na yi karatun addini, amma da na fara sai na ji kamar raina ba ya so, a bani shawara nagode

Amsa :

Wa alaikum assalam.To dan'uwa akwai abubuwan da suke taimakawa wajan samun ilimin addini, ga muhimmai daga cikinsu:

1. Tsarkake niyya- duk lokacin da ka tsarkake niyyarka wajan neman ilimi, to Allah zai taimakeka.

2. Yin aiki da abin da mutum ya karanta- domin yin aiki da ilimi yana daga cikin abubuwan da suke taimakawa wurin rike ilimi da kuma kiyaye shi.

3. Neman taimakon Allah – saboda ana so mai neman ilimi ya dinga tunawa cewa Allah shi ne MASANI mai sanar da kowa, don haka ya dinga neman taimako a wurinsa yana rokonsa ya buda masa basira.

4. Nisantar zunubai, saboda ilimin addini haske ne, kuma hasken Allah ba ya bawa mai sabo.

5. Yawan maimaitawa, domin maimaita ilimi na daga cikin abubuwan da suke taimakawa wajan samun ilimi da tabbatarsa a zukata .

6. Jure wahala da kuma hakuri , saboda neman ilimi ba ya yiwuwa sai da wahala kuma duk wanda ba zai iya jure wahala ba, zai yi wuya ya iya neman ilimi yadda ya kamata.

7. . Farawa da abin da ya dace da dalibi, domin ana so dalibi ya fara da littafin da ya dace da shi wurin neman ilimi, saboda idan ya fara da littafin da ya wuce matakin karatunsa, ba zai fahimce ba.

Ina tabbatar maka mutukar ka rike wadannan to Allah zai taimakeka, ka samu ilimi cikin kwanciyar hankali

 Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

26/4/2014

 

191. TAMBAYA

WURAREN DA YA HALATTA A SAKI MACE MAI HAILA!

 

Assalamu alaikum.

Akaramakallah na ji an ce haramun ne a saki mace mai haila, to amma wani lokacin za ka ga kun samu rashin jituwa da matarka ta yadda ba za ka iya jiran lokacin tsarkinta ba, to malam ko akwai wasu lokuta ne da aka halattawa mutum ya saki matarsa ko da tana haila ?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa tabbas Allah ya yi umarni da kar a saki mace sai tana da tsarki kamar yadda yake cewa "Idan za ku saki mata to Ku sake su a farkon iddarsu) ma'ana a tsarkin da ba ku take su ba, Addalak aya ta : (1) saidai akwai wurare guda hudu da ya halattta a saki mace mai haila :

1.Idan sakin ya kasance kafin ya kadaita da ita ko kafin ya sadu da ita, to anan ya halatta ya sake ta tana haila.

2. Idan ta yi hailar ne tana da ciki.

3. idan ya sake ta ne bayan ta fanshi kanta, to anan ya halatta ko da tana haila, saboda Annabi s.a.w. bai tambayi matar Thabit ba shin tana haila ne ko tana da tsarki, lokacin da zata yiwa mijinta kul'i, kamar yadda Bhukari ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 5273.

4. Idan watanni hudu suka cika a lokacin ila'i, to ko da tana haila zai iya sakinta.

Don neman karin bayani duba : Dima'uddaabi'iyya shafi na :33

In ban da wadannan wurare, to bai halatta a saki mai haila ba, kuma yin har an sake ta, to sakin bai auku ba a wajen wasu malaman.

Allah ne mafi sani.

Dr.Jamilu Zarawa

27/4/2014

 

192. TAMBAYA

SHIN BAIKO AURE NE?

 

Assalamu alaikum,

Malam an yi min baiko da wani mutum, to shi ne zai yi tafiya sai ya biyo ta gidanmu wai yana so mu sadu, ya yi ta kawo min kauli-da-ba'adi, akan cewa, ai mun riga mun yi aure, ni dai gaskiya malam na ki yarda saboda ina da shakka akai, shi ne nake neman fatawa ?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa tabbas akwai malaman da suka yi fatawa a Nigeria cewa : baiko aure ne, saidai zance mafi inganci shi ne baiko ba aure ba ne saboda hujjoji kamar haka :

1. Abin da aka sani shi ne kudin da ake bayarwa yayin baiko ba'a bada su da nufin sadaki, duk da cewa wasu suna dunkulewa su bayar gaba daya, kin ga kuwa in haka ne, to ai dukkan aiyuka ba sa ingatuwa sai da niyya, kamar yadda ya zo a hadisni da dukkan malaman hadisi suka rawaito.

2. Bayan an yi baiko mutum zai iya cewa ya fasa, a dawo masa da kudinsa, kin ga wannan yana nuna ba aure ba ne.

3. Hakan zai iya bude hanyoyin barna, don dukkan wani ashararu zai iya kai kudi a yi masa baiko da wacce yake so ya yi lalata da ita, addinin musulunci kuma ya haramta duk abin da yake kaiwa zuwa barna.

4. Yana daga cikin sharudan auren a wajan wasu malaman samun shaidu, kin ga kuwa wani lokacin wanda zai kai kudin da za'a yi baiko, zai iya zama mutum daya, kin ga akwai nakasu kenan.

5. Abin da muka sani a kasar Hausa, sai bayan an yi baiko, ake sanya ranar daurin aure, kin ga wannann yana nuna cewa, baiko daban, aure daban.

6. Sannan duk  mun yarda cewa baiko ba ya wajabta gado  tsakanin wadanda aka yiwa, idan daya daga cikinsu ya mutu  kin ga wannan yana nuna cewa ba aure ba ne, domin ma'aurata suna gadon junansu.

Allah ne mafi sani.

24/3/2014

Dr. Jamilu Zarewa

 

193. TAMBAYA

BAMBANCI TSAKANIN RIIBA DA RIBA

 

Assalamu alaikum, malam

Don Allah ina da tambaya? wai miye riba a musulunci? kuma idan mutum ya siyi abu nera 5 ya halatta ya sai da akan nera 8?

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To malama riba ta kasu kashi biyu :

1. Akwai ribar jinkiri, kamar ka ba mutum bashin naira hamsin, ka nemi ya dawo maka da naira sittin, ko kuma idan ka bawa mutum bashi, ya yi jinkirin biya, ka ninninka masa kudin da ka ba shi, irin ribar da ake amsa a banki, za ta shiga cikin wannan bangaren.

2. Ribar fi-fiko, kamar yanzu, ki bada naira 1100 tsofafi, a ba ki naira 1000 sababbi, ko kuma ki bayar da shinkafa 'yar gwamnati kwano uku, a ba ki shinkafa ta gida kwano hudu.

Duka wadannan nau'oin guda biyu Allah ya haramta su, kuma ya kwashe musu albarka.

Amma idan mutum ya sayi abu naira 5, ya sayar naira 8, wannan ba'a kiran shi riba a musulunci, saboda yana daga cikin riibar da Allah ya halatta, saidai ana so mutum ya saukaka idan yana siyar da kaya, Annabi s.aw. yana cewa : "Rahamar Allah ta tabbata ga mutumin da idan zai siyar da kaya yake rangwame.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr Jamilu Zarewa

24/4/2013

 

194. TAMBAYA

ZAN AURI MA'AIKACIN BANKI, AMMA INA TSORON CIN HARAM?

 

Assalamu Alaikum, Dr. Akwai wata kanwata da wani ma'aikacin banki yake so ya aura, ta bangaren mu'amalarsa za mu ce Alhamdulillah, to shi ne take neman menene halarcin auransa a shari'a? Saboda tana tsoron kar ya rika ciyar da ita da dukiyar haramun.  

Amsa

Wa'alaykumussalam,

 To dan'uwa Annabi  s.a.w.  yana cewa : "Allah ya la'anci mai cin riba da mai rubutata, da wadanda suka yi shaida akan haka" Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 1598.

Hadisin da ya gabata yana nuna haramcin aiki a bankunan da suke mu'amala da riba, saboda ma'aikacin banki zai rubuta ko kuma ya shaida, ko ya taimaka wajan tsayuwar harokokin banki, kamar mai gadi, da dan aike...

Duba fatawaa Allajanah adda'imah 15\41, da Fataawaa Islamiyya na Ibnu-uthaimin 2\401.

Idan ya zama abin da ma'aikacin banki yake amsa haramun ne, kuma ba shi da wata sana'a sai wannan, akwai hadari a auransa, saboda zai ciyar da matarsa da haramun

 Malamai suna cewa duk mutumin da yake samun kudi ta hanyoyin halal da haram, idan ya maka kyauta za ka iya amsa,  saboda Annabi s.a.w. ya yi mu'amala da yahudawa, kuma a dukiyarsu akwai halal da haram, amma in ba shi da wata sana'a sai ta hanyar haram to ba za ka iya cin dukiyarsa  ba.

Wasu malaman sun halatta aikin banki a bankuna masu kudin ruwa da niyyar kawo gyara, idan niyyar mutum ta tsarkaka. 

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Zarewa

10\4\2015

 

195. TAMBAYA

MAHAIFIYATA TA RASU, ANA BIN TA AZUMI, YA YA KAMATA MU YI?

 

Assalamu alaikum, Malam dan Allah ina da tambaya? tun kafin a kama azumi uwata ba ta da lafiya har akayi sallah, rana ta 16 ga watan karamar sallah  Allah yayi mata rasuwa, shin za mu ranka mata azumi ko ba sai mun ranka ba ? Allah ya saka da hairi.

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To malam mutukar rashin lafiyar ta zarce mata, har zuwa lokacin mutuwarta, to ba za ku rama mata ba, tunda ba sakaci ta yi ba, saboda fadin Allah madaukaki  :  "Kuma duk wanda yake mara lafiya ko matafiyi to sai ya rama a kwanaki na daban" Bakara aya ta : 185, wato bayan Ramadahana, idan mara lafiya ya samu sauki, ko matafiyi ya dawo , Ka ga wanda bai samu sauki ba har ya mutu, zai zama bai kai lokacin da zai rama ba, don haka sai ya saraya akan shi.

Amma idan ta samu damar ramawa,  ta yi sakaci ba ta rama ba har ta  mutu, to sai makusancinta ya rama mata, saboda fadin Annabi s.a.w.  : "Duk wanda ya mutu akwai azumi akansa, to sai makusancinsa ya rama masa" . kamar yadda Bukhari ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta: 1851. Duba Fataawa nuru aladdarb lamba ta : 247.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr.Jamilu Yusuf Zarewa

1\11\2014

 

196. TAMBAYA

YAUSHE NE LOKACIN SALLAR WALAHA?

 

Assalamu alaikum. Malam daidai wanne lokaci  ne ya da ce a bisa kiyasin lokacin ayi sallar walaha?

Amsa

Wa alaikum assalam,

To malam lokacin sallar walaha yana farawa ne daga sanda rana ta daga ta fara zafi, kamar yadda Annabi s.a.w. yake cewa a cikin hadisin Muslim mai lamaba ta : 748 "Sallar walaha lokacin da 'ya'yan rakuma suka fara jin zafi" sannan lokacin yana karewa dab da zawalin rana, da minti sha biyar ko kusa da haka.

Allah ne mafi sani.

25/2/2014

Dr. Jamil Zarewa

 

197. TAMBAYA

WANDA YAKE GIDA, ZAI IYA HADA SALLOLI SABODA RUWAN SAMA?

 

Assalamu alaikum Allah ya karawa

malam ilimi da fahimta. Shin da Allah malam ko mutum zai iya hada sallah shi kadai idan ana ruwa bashi da ikon zuwa masallaci?. Nagode malam.

Amsa

Wa alaikum assalam. To dan’uwa malamai sun yi sabani akan wannan mas’alar zuwa maganganu guda biyu :

1. Ya halatta ga wanda yake a gida ya hada

salloli saboda ruwan sama, tun da ruhusa ce Allah ya bawa mutane, don haka ta shafi kowa

da kowa, wannan ita ce maganar Hanabila

kamar yadda Mardawy ya ambata a INSAAF

2\340.

2. Bai halatta ga wanda bai je sallar

jam’i ba ya hada salloli saboda ruwan sama,

saboda an yi sauki ne ga wadanda za su je

masallaci don kar su jika jikinsu da ruwa,

wannan wahalar kuma babu ita ga wanda ya yi sallah a gida, don haka rahusar baza ta sameshi ba, sannan kuma shari’a ta yi nufin ta kiyaye sallar jam’i shi ya sa ta saukaka wajan hada

salloli a ruwan sama,don kar mutane su watse sallar jam’i ta tozarta, wannan ita ce maganar

Imamu shafi’i a littafinsa Al’umm 1\195, Afahimtata maganar karshe ta fi inganci, don haka wanda yake gida ba zai hada salloli ba.

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR JAMILU YUSUF ZAREWA

12/11/2015

 

198. TAMBAYA

ZAN IYA RIKE HANNUN BUDURWATA?

 

Assalamu alaikum,

Malam Ya Hukunchin Wanda ya rike Hannun wata mace Kuma ba matarsa ba ce, amma Budurwarsa ce?

Amsa

Wa alaikumus salam,

Bai hallata mutum ya rike hannun wacce ba muharramarsa ba, kuma ba matarsa ta aure ba. Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance ba ya Musafaha (hada hannu) da mata yayin da zai musu mubaya'a, yana yi musu mubaya'a ne da Magana, kamar yadda ya tabbata a hadisi.

Taba hannun budurwa hanya ce da take kaiwa zuwa ga Zina saboda yana tayar da sha'awa, Allah Madaukaki ya haramta kusantar zina a aya ta 32 a suratul Isra'i, Zina tana daga cikin manyan zunuban da babu kamar su bayan shirka da Allah.

Wanda ya kiyaye dokokin Allah, tabbas Allah zai kiyaye shi, wanda ya bı son zuciyarsa, to Allah yana nan a madakata.

Allah ne mafi sani.

Dr Jamilu Zarewa

05/05/2016.

 

199. TAMBAYA

SHIN ZAN IYA NEMAN SAKI DON MIJINA BAYA HAIHUWA...!!

 

Assslam alaika warahamatullah

Dr inada matsala kamar haka fatan za'a taimakamin da amsa malam munyi aure da mijin yau kusan shekara goma muna tare amma Allah bai bamu haihuwa ba sannan kuma dan uwa nane na jini gashi yanzu banason zama dashi shin idan na nemi ya sawwakemin nayi laifi?

Kuma hakan na nuna cewa nakasa cinye jarrabawar da Allah yayimin kenan?

AMSA

Wassslam Alaiki warahamatullah wabrakatuhu

To yar uwa shi asalin aure a musulunci yana daga cikin manufofinsa shine samun zuri'a ma'ana yaduwa a samu al'ummah

Annabi s.a.w. yace kuyi aure Ku domin Ku samu zuri'a kuma ku auri matayen da kukeso masu haihuwa ni zanyi alfahari da yawanku wajan yawan al'umma ranar alkiyama

To yar uwa bazan ce dake ki rabu dashi ba shawarata gareki shine kiyi hakuri ki yawaita addu'oi wata kila Allah ya baku haihuwar nan gaba amma idan kinga shekarun da kukayi sunyi yawa sunyi miki yawa ba zaki iya cigaba da zama dashi ba bakwa haihuwa zaki iya neman ya sawwake miki amma badon kunyi fada ba kuyi rabuwar lami lafiya to babu laifi shima ya kamata ya sawwake miki amma yar uwa ki sani cewa ba'asan matsalar daga gareki take ba ko daga garesa ne kada sai bayan kun rabu a gane daga gareki ne matsalar

Allah shine mafi sani

Dr. Abdallah Gadon kaya

11~2~2017

 

200. TAMBAYA

LAULAYIN CIKI YASA INA WAIWAYE A SALLAH?

 

Assalamu alaikum malam Dan Allah macece take fama da yawan zuban yawu a bakinTa na laulayin ciki, Wanda yakai kafun nayi raka'a daya ya cikamun baki sai na dan juya in zuba akan tsumma, sallan yayi ko bani da halin juyawa kadan?

Amsa

Wa alaikum assalam. To 'Yar'uwa Annabi s.a.w. yana cewa : "Waiwaye a sallah wani faucewa ne da Shaidan yake fauta daga sallar bawa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lambata : 718.

Malamai suna cewa waiwaye a sallah makaruhi ne saboda hadisin da ya gabata.

Waiwaye yana halatta idan akwai bukata, saboda akwai lokacin da  sayyidina Abubakar ya fara limanci, saboda Annabi s.a.w. baya nan, bayan  Annabi s.a.w. ya dawo sai ya shigo masallaci, sahabbai suna ganinsa sai suka fara tafi, sai sayyadina Abubakar ya waiga lokacin da ya ji tafi ya yi yawa" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2544.

Malamai suna cewa : waiwayan da Abubakar ya yi yana nuna hallacin yin waiwaye saboda bukata, tun da Annabi s.a.w. bai masa inkari ba.

Don neman karin bayani duba : Fataawaa nurun Aladdarb 9\225.

A  bisa abin da ya gabata, ya hallata ki dinga yin waiwaye saboda  zubar da yawun da ya zama lalura, saidai duk abin da aka halatta saboda bukata, ba'a so a wuce gwargwadonta.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREAWA

19\4\2015


No comments: