GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Sunday 4 September 2022

TAMBAYA TA DARI UKU DA ASHRIN DA DAYA (321) ZUWA TA DARI UKU DA ARBA'IN (340)

321. TAMBAYA

MAI TAKABA ZATA IYA FITA SALLAR IDI?

 

Assalamu alaikum warahmatullah, Barka da war haka. Don Allah YA halatta me takaba ta je sallar Eid?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Bai  halatta ga mai takaba ba ta  fita zuwa Idi, saboda Hadisin  Ibnu Majah Mai lamba ta: (2031)  inda Annabi SAW yake cewa da  Furaia lokacin da mijinta ya Rasu: (Ki zauna a cikin  gidan da  kika samu labarin mutuwar mijinki har zuwa Ki kammala iddarki"

Hadisin da ya gabata yana nuna cewa: Mai takaba

ba za ta fita ba sai in akwai lalura, sallar idi kuma ba ta cikin lalorori a sharia.

Imamu  Ashshaukani a cikin Nailul Audaar 3/343 ya yi bayani cewa "Dukkan Mata ana fitar da su daga gidanjansu Don su halarci idi, in ban da wacce take iddar mutuwa.

Allah ne mafi Sani

Dr. Jamilu Zarewa

03/09/2017

 

322. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum

Malam me hukuncin wanda ya qara gashi akansa irin wanda maza suke zuwa ana musu surgery ashuka musu gashin musamman ga masu sanko ko kuma waenda gashin kansu ke cincinyewa wai saboda su zama dai dai da sauran

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

Bai  halatta ga namiji ya kara gashi ba,  saboda hakan canza halittar Allah ne.

Kasancewar Allah ya haramtawa mata kara gashi a cikin hadisai ingantattu duk da cewa suna tasowa NE a cikin kwalliya kamar yadda ayar Suratu Azzukruf ta tabbatar, hakan sai ya nuna namiji ne ya fi cancanta da haramcin, tun da shi ba'a  yi shi don Ado ba.

Malamai suna cewa duka nassoshin da suke haramtawa mata kara gashi, to maza ma suna ciki,  amma an kebance mata ne da haramcin saboda su ne suka fi yawan aikatawa.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

03/09/2017

 

323. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum dr. Ina maka fatan alheri da fatan anyi sallah lfy don Allah dr. ina da tambaya kamar haka? Mutum ne ya mutu ya bar mace da yara maza 9 da mata 12 da kudi naira miliyan daya da dubu dari to malam ya kason zai kasance Allah ya kara lfy Allah yasa kayi hajjin mabruor.

Amsa

Wa alaikum assalam, Za'a raba kudin gida takwas, sai a bawa matar mamacin (137,500), ragowar (962,500) sai aka sa su gida talatin kowanne namiji ya dau kashi biyu, tun da su tara ne, kowacce mace ta dau kashi daya tun su (12).

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

06/09/2017

 

324. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum, mutum ne yake cikin halin rashin lafiya, kuma al'ummah da suke tare ba masu taimakawa ne ba,gashi wannan ciwon nason ya hallaka shi, shi kuma ba shi da kudi kuma ba shi da hanyar kudi, malam shin zai iya karbar kudin LOAN na govt don surika cirewa duk wata, ko babu halin haka nagode Allah yakara karfin imani da basirah

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Ya halatta ya amshi rancen mai ruwa, mutukar abin da yake damunsa, ya kai wancan halin da ka ambata, saboda larura tana halatta abin da aka hana, saidai ya wajaba ya amsa gwargwadon bukata .

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

3\6\2015

 

325. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum.Don Allah malam ya matsayin mutumin da ya sha nonon matarsa,  ya aurensu  yake ?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa Allah madaukakin sarki ya halatta maka jin dadi da dukkkan bangarorin jikin matarka, in ban da dubura ko kuma saduwa da ita lokacin da take haila,  don haka  ya halatta ka tsotsi nononta mutukar babu ruwa a ciki, amma idan akwai ruwa a ciki, to malamai sun yi sabani akan halaccin hakan zuwa  maganganu guda biyu :

1. Ya halatta, saboda kasancewar nonon da yake haramta aure shi ne wanda aka sha kafin yaro ya cika shakaru biyu,  saboda fadin Annabi s.a.w. "Shayarwar da take haramtawa, ita ce wacce yaro ya sha saboda yunwa" , Bukhari lamba ta : 5102,  ma'ana lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono, saboda shi ne abincinsa, shi kuma wannan ya faru ne bayan mutum ya girma don haka ba zai yi tasiri ba wajan haramta aure,  wannan ita ce maganar mafi yawan malamai.

 

2. Bai halatta ya sha ba, saboda ko da yaushe mutum ya sha nonon mace to ta haramta a gare shi, domin Annabi s.a.w. ya umarci matar Abu-huzaifa da ta shayar da Salim,  don ta haramta a gare shi, kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2636, tare da cewa a lokacin Salim ya riga ya girma,  wannan sai yake nuna cewa idan babba ya sha nono to zai yi tasiri wajan haramcin aure.

Zancen da ya fi karfi shi ne ya halatta miji ya sha nonon matarsa, saidai rashin shan shi ne ya fi, saboda fita daga sabanin malamai yana da kyau.

 Don neman Karin bayani duba : Bidayatul-mujtahid 2\67

 Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

1\11\2014

 

326. TAMBAYA

 

Assalamu Alaikum.

Don Allah ataimake ni akan wannan tambayan, mutum ne yarasu bashi da kowa sai mahaifinsa da kaninsa 1 Da kannansa mata 2 ,toh ya za'ai masu rabon gado?

Amsa

Wa alaikum assalam,

Mahaifinsa ne zai cinye dukkan dukiyar.

'Yan'uwan mamaci ba sa gado mutukar akwai Ubansa yana raye.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

11/09/2017

 

327. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum. malam don Allah ina da tambaya da fatan za'a amsamin, wai mutum zai iya rabawa iyalansa gadansa kafin yamutu wai hakandin ya halatta? nagode

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan'uwa malamai suna cewa hakan bai inganta ba, saboda dalilai, ga wasu daga ciki :

1. Hakan yana daga cikin gaggauta abin da Allah ya jinkirta, saboda Allah ya sanya rabon gado ne, bayan mutuwa.

2.  Zai iya yiwuwa daya daga cikin  iyalan nasa ya mutu kafin shi, ka ga sai a samu kwan-gaba kwan-baya.

3. Yana iya jawo hassada saboda daya daga cikin magadan zai iya yin kasuwanci da gadon da aka ba shi ya samu riba mai yawa kafin magajinsa ya mutu, wanda hakan zai iya kawo hassada tsakanin magada, don za su ga da ba'a yi gaggawar rabawa ba da ya kasance daga cikin rabonsu.

4. Yana daga cikin sharudan gado tabbatar da mutuwar  wanda za'a gada .

 

Allah ne mafi sani 

Dr. Jamilu Zarewa

6\7\2015

 

328. TAMBAYA

 

Assalam alaikum malam ina da tambaya; misali ni brikilane kuma na kasance musulmine sai aka ban contrc din gini na church, ogana ya ce mu za muyi; yaya matsayin mu yake idan munyi wannan aikin?

 

Amsa

Wa alaikum assalam To dan'uwa  malamai sun yi bayani cewa : bai halatta musulmi  ya zama Birkila a  Chochi ba, saboda hakan yana daga cikin taimakawa aikata zunubi, kuma zai iya jawowa mutum ya ga yadda ake shirka da Allah, wanda hakan zai  iya masa tasiri.,

Allah madaukaki yana cewa " kada ku yi taimakekeniya wajan aikata  sabo", " suratul Al-maidah aya ta : 2, sannan duk abin da yake kaiwa zuwa barna, to zai zama haramun ko makaruhi.

Don neman kari bayani duba : Al'umm ta Shafi'i    4/213.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

19\5\2015

 

329. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum waraha matullah.malam mijina ne ya rasu ya barmu da abukiyar zamana da yara ukku mata da mahaifiyarshi inda yabar gida da mota malam ya hukuncin rabon gadon yake nagode

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Za'a raba abin da mijinku ya bari gida (24), a bawa 'ya'yansa mata kashi (16), mahaifiyarsa kashi (4) ku kuma matansa a ba ku kashi (3) ku raba, ragowar kashi dayan sai a bawa wanda yafi kusa da mijinku daga mazan da sharia ta tabbatar suna gado .

In kuma babu sai a yagalgala shi a tsakaninku.

 

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

16/09/2017

 

330. TAMBAYA

 

Assalama alaikum. Malam dan Allah

Ina aiki ne  akarkashi wani Alhaji Amman a nazargin sa da wai  kudisa bana halal bane wasu suce dan  luwadi ne  wasu  kuma suce kudin lukudu ne ina  so insan  yadace nacigaba damai aiki ko inbari Allah y kara lpy da ilimi da kafin basira ameen

 

Amsa

Wa alaikum assalam, Ya wajaba ka tabbatar da hakan kafin ka yanke hukunci.

Ba'a gina hukunci a musulunci akan shakka ko zato mara rinjaye, saboda wani sashen zaton zunubi ne kamar yadda aya ta (12) a cikin suratul Hujraat ta tabbatar da hakan.

Idan wani bangare na kasuwacinsa halal ne wani kuma Haram ne za ka iya hulda da shi, saboda Annabi S.a.w. ya yi mu'amala da yahudawa kuma a cikin dukiyarsu akwai halal akwai kuma haram.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

16/09/2017

 

331. TAMBAYA

 

Assalam Alaikum.

Malam, menene hukuncin amfani da *LAYA KO GURU a musulunci?

 

Allah yasa mu dace.

Amsa

Wa alaikum assalam,

To dan'uwa Layu da guru sun kasu kashi biyu:

1. Layun da aka yi su da Sakandami ko Hatimi ko sunayan aljanu ko wani abu na daban wanda ba Qur'ani ba, wannnan malamai sun cimma daidaito game da haramcinsu kamar yadda ya zo a Fataawaa Allajna Adda'imah 2/212 saboda fadin Annabi S.A.W. (LAYU da kuma abin da ake daurawa mace don miji ya sota shirka ne) kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (3883) kuma Albani ya inganta shi, sannan da hadisin da Imamu Ahmad ya rawaito mai lamba ta: (16969), inda Annabi S.A.W. yake cewa: (Wanda ya rataya laya to ya yi shirka, shima wannnan hadisin Albani ya inganta shi a Silsila Sahiha.

Hadisan da suka gabata suna nuna haramcin daura Laya saboda Manzon tsira ya kira ta da shirka, shirka kuma tana fitar da mutum daga musulunci.

2. LAYUN da aka yi su daga Alqur'ani ko hadisai ingantattu, wadannan na'u'i malamai sun yi sabani akansu:

A. Sun halatta saboda sun kunshi sunan Allah da kuma karatun alqur'ani wanda sifar Allah ce, wanda ya dogara da su ya dogara ga Allah, wannan ita ce maganar Amru bn Al-ass da Aisha da wasu daga cikin magabata.

B. Ba su halatta ba saboda Ba'a samu Annabi S.A.W. ya yi ba, da hakan sharia ne da an gan shi ya yi ko da sau daya ne a rayuwarshi, sannan rataya layun da suke dauke da Alqur'ani zai jawo a wulakanta su tun da za'a shiga wurare marasa tsarki da su lokacin biyan bukata, kiyaye hakan kuma yana da kamar wuya.

Zance mafi inganci shi ne haramcin amfani da Layun da suke daga Alqur'ani saboda dukkan alkairi yana cikin biyayya ga manzon Allah S.A.W, sannan shariar musulunci ta halatta mana addu'o'i da yawa na neman kariya wadanda suka wadatar da mu daga layu.

 

Allah ne mafi sani.

Don neman karin bayani duba: Taisirul Azizil Hamid shafi na : (136) da kuma Ma'arijul Kabul 2/510

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

4/10/2017

 

332. TAMBAYA

Assalamu alaikum

Don Allah Malam wata tambaya aka yi min, shi ne na ke son a taimaka min wajan ba da amsa, tambayar ita ce : me ya kamata mai yaron ciki ta kula da shi ?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To malama akwai abubuwan da ya kamata mace ta kula da su, lokacin da take da ciki, ga wasu daga ciki :

1. Ki yi kokari, ki dinga cin halal, saboda lokacin da yaro yake ciki, na daga cikin lokutan da yaro yake ginuwa, don haka, idan kina cin haramun, yaron zai ginu da ita, sai Allah ya fara cirewa gabobinsa son alkhairi, tun yana yaro, domin duk jikin da ya ginu da haramun zai zama mai kasala wajan aikata abin da Allah yake so, kamar yadda malamai suka yi bayani.

2. Wasu malaman suna cewa : yawan saduwa yana karfafa yaro a ciki, saboda Annabi s.a.w ya kamanta ciki da shuka, kamar yadda ya zo a hadisin Abu dawud, mai lamba ta :  1847, kuma shuka tana kara karfi duk lokacin da aka bata ruwa.

3. Neman masa tsari daga shaidan, kamar yadda mahaifiyar nana Maryam ta nemarwa 'yarta tsari, lokacin da ta haife ta.

4. Nisantar duk wani abu da zai cutar da shi, saboda musulunci ya yi umarni da kula da rai, don haka zai yi kyau a matsayinki na sabon aure, ki nemi shawarar magabata da kuma likitoci, saboda ki gujewa abin da zai cutar da yaronki.

5. Zuwa asibiti, lokaci-lokaci don tabbatar da lafiyar yaron.

ALLAH SHI NE MAFI SANI.

Dr. Jamilu Zarewa

16\6\2014

 

333. TAMBAYA

Assalamu Alaikum

 malam AWAL ga tambayata kamar haka minene hukuncin wanda yatararda liman Acikin sallar Isha sai yasami  raka biyu nakarshe idan zaikawo cikon raka watarana yakan bayyana karatun fatiha da sura batareda yayi Ba,adiyaba ko Qabliyya shima yaya hukuncinsa yake?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

Wato an samu sabani ne tsakanin malamai wajen wanda ya samu raka'o'i biyun karshe tare da liman, shin sune na farkon sa ko kuwa sune na karshen sa shima, wadan da sukace abinda ya samu sune na farkon sa kaga kenan zai ciko biyun karshe a yadda suke wato fatiha kawai kuma a asirce, amma wadan da suka ce abinda ya samu sune na karshen sa toh kaga zai rama biyun da suka wuce shi kenan, a yadda suka wuce shi wato fatiha da sura kuma a bayyane dukkan ma'abota wadannan maganganun suna da madogara daga abinda suka fahimta na hadisan manzon Allah, amma abinda yafi rijaye wajen malamai shine maganar farko wato abinda ya samu sune na farkon sa don haka zai cika abinda ya rage masa, wato zai karanta fatiha kawai a boye a duk raka'o'in biyu.

Wannan shiyafi dacewa da fadar manzon Allah...

ما أدركتم فصلوا وما فاتكم فأتموا...

Duk abinda kuka riska ku sallata kuma Abinda ya wuce ku sai ku ciko..

Wallahu A'alam.

Malam NURUDDEEN MUHAMMAD(MUJAHEED)

26/09/2017

 

334. TAMBAYA

Assalamu alaikoum malam muna so a fidda mu cikin shakku. Manzon Allah SAW ya hana ayi azumin nafila a ranar Asabar toh yaya zamuyi? ayi mana bayyani game da azumin assabar na tasu'a

Za mû yi shi ko kuma tsallakeshi za mû yi saï mû azumci ranar ashura lahdi?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

Babu komai zaku iya yin azumin ku, hanin dake cikin Hadisin Abdullahi bin Busrin al'maziny na kada ayi azumi ranar asabar malamai sun kebance shi da halaccin yi saboda hadisai masu yawa daga cikin su akwai hadisin Abu Huraira wanda ke cikin Bukhari ( kada kuyi azumi ranar Jumma'a saifa in kun hada da na yinin kafin Jumma'a din (wato alhamis kenan) ko yinin bayan Jumma'a din (wato asabar kenan)

Da kuma hadisin Juwairiyya, wanda manzon Allah ya shigo wurin ta ranar Jumma'a sai ya tarar tana azumi sai ya tambaye ta kinyi na jiya tace a'a sai yace zakiyi na gobe sai tace a'a sai yace to in haka ne ki karya azumin ki...

Da ire iren wadannan hadisan malamai suka ce hanin ya shafi kebance ranar asabar din ne ita kadai.

Amma idan za'a hada da wata rana toh babu laifi,

Imam Ibn Kudaama a cikin littafin sa Al'mugni yace makaruhi ne kebance ranan asabar da zumi amma in za'a hada da wata ranar toh babu karhanci.

 

Wallahu A'alam

Malam Nuruddeen Muhammad (Mujaheed)

26/09/2017

 

335. TAMBAYA

Assalamu alaikum.

Shin idan miji ya saki matarsa sai bayan mako biyu Allah ya yi masa rasuwa zatayi takaba?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

Macen da mijinta ya sake ta kafin ta kammala idda sai mijin ta ya rasu, malamai sunyi maganganu uku:-

(1) ya zamanto sakin akwai kome a cikin sa wato saki daya ko biyu, toh malamai sunyi ittifaqi zata fita daga idda ta koma takaba kuma tana da gado, domin mace matukar tana cikin idda bata fita daga hurumin mijinta ba don haka ma yana da ikon dawo da ita ba tare da andaura aure ba, don bata halatta ga wani sai bayan idda.

(2) ya zamanto sakin babu kome a cikin sa kamar saki uku kuma mijin yayi sakin a lokacin yana lafiya lau, toh a wannan hali ba zata ci gado ba bisa ijma'in malamai sunce domin alaqar dake tsakanin su ta yanke.

(3) ya zaman toh sakin babu kome a cikin sa wato saki uku amma a lokacin sakin mijin yana kwance ba lafiya/yana jinya (ciwon ajali) ya zamanto nufin mijin shine haramta wa matar cin gado toh a irin wannan matsalar malamai sunyi sabani:

* Mazhabar imam A shafi'i sunce ba tada gado / ba zatayi takaba ba.

* Mazhabar Abu hanifa sunce tana da gado/takaba matukar tana cikin idda hakan ta faru.

* Mazhab na Imam Ahmad bin hambal suce za taci gado/takaba matukar ba ta auri wani mijin na daban bane.

Aduba littafin (Al'mugni 9/194-196)

Da yawa daga cikin malaman wannan zamann sun tafi akan ra'ayin mazhabar iman Ahmad kamar irin su Sheikh Bin Bazz da Sheikh Ibn Usaimeen da Sheikh Swaleh fauzan da sauran su...

A duba ( Fawa'idul Jaleelah Fil mabaahithul Fadiyya na Sheikh bin bazz Shafi na 6) da (tahkikatul Fardiyya Fi mabaahithul fardiyya na Sheikh swaleh fauzan shafi na 33- 36).

Wallahu A'alam

Malam Nuruddeen Muhammad (Mujaheed)

28/09/2017

 

336. TAMBAYA

Assalamu Alaikum, mutum musulmi zai iya shiga chikin church domin halartar aure na aboki ko abokiyar karatun sa?

 

Amsa

Wa alaikum assalam

Yawanci auran Crista a wannan zamanin ba ya rabuwa da kade-kade da raye-raye, da roko da Neman albarka a wajan Jesus a matsayinsa na Allah a Wajansu, da Addu'o'i Wadanda suka sabawa koyarwar addininmu.

Wannan ya sa barin halartar ya fi dacewa da sharia.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

05/10/2017

 

337. TAMBAYA

Assalamu Alaikum Dr. dan Allah inada tambaya akan matar da keda ciki yakai wata hudu sai jini ya rinka xubar mata daga baya kuma sai ya dauke bayan kwana guda ko biyu yakan iya dawowa ko bayan wasu awoye shin ya hukuncin sallar ta? xata jinkirta sallah sai jinin ya dauke ko xata rika yin wanka duk sanda ya dauke tayi rankon sallolin baya ne. 

Nagode

 

Amsa

Wa alaikum assalam To 'yar'uwa mutukar cikin ya kai wata hudu kuma jinin da yake fita yana hade da ciwon haihuwa, to ya zama jinin biki, kuma zai hana sallah, amma Idan babu ciwon haihuwa to mutukar ya zo da sifar jinin haila (baki ko karni) to zai zama haila, tun da a zance mafi inganci mai ciki tana iya yin haila.

In ya fita daga wadannan biyun zai zama jinin cuta ta yadda ba zai hana sallah ba, in har jinin kusa-kusa yake fita, za ki iya jinkirta salloli, sai ya dan tsagaita, sai ki rama sallaolin da aka yi su kina da tsarki, saboda addinin musulunci addini ne mai sauki, babu kunci da damuwa a cikinsa, kamar yadda aya ta karshe a suratu Al-hajj ta yi bayanin haka.

Allah ne mafi Sani. 

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

03/02/2016

 

338. TAMBAYA

Assalamu Alaikum

 Tambaya daga jahar Taraba Suna so Dr ya amsa musu a wannan zaure mai albarka.

Wata ce take da Miliyan daya tana so tafir da zakka nawa ne ya kamata ta fitar dashi?

Allah ya tsare mana Dr ya yi mashi sakamako da gidan aljannah fiddaus.

 

AMSA

Wa alaikum assalam,

 Idan ta mallaki miliyan daya (1,00000), kuma su ka yi shekara daya a wajanta, to za ta fitar da dubu ashirin da biyar (25,000), wato daya cikin arba'in din abin da ya mallaka.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

10/10/2017.

 

339. TAMBAYA

Assalamu alaikum, Mallam Na kasance ina tsotsan azzakarin mijina, shi kuma yana wasa da gabana da harshensa kafin mu sadu, ina matsayin haka a addinin musulunci.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To 'yar'uwa hakan ya halatta, ba matsala a sharian ce, saboda an rawaito halaccin haka, daga magabata, daga cikinsu akwai Imamu Malik, saidai ya wajaba a tabbatar an tsaftace wurin musamman farjin mata, saboda a bude yake, sannan kuma wuri ne da ake yin haila, ake kuma zuba maniyyi, ga shi kuma yana kusa da wajan yin bahaya, wasu masana likitanci suna bada shawarar cewa : a dinga wanke wurin da gishiri kafin a tsotsa, saboda neman kariya

Allah madaukakin sarki a cikin suratul Bakara aya ta : 223, ya kwatanta mace ga mijinta da gona, wannan sai ya nuna dukkan bangarorin jikinta ya halatta a ji dadi da su, in ban da cikin dubura wacce nassi ya togace.

Allah ne mafi sani.

Duba : Mawahibul-jalil sharhin Muktasarul Khalil  3\406,

 

Dr. Jamilu Zarewa

  20/12/2014

 

340. TAMBAYA

 

Assalamu alaikum.

yaa shaikh (dr.) mutun ne Allah ta'ala ya bashi karuwa ta (haihuwa) bai samu hali yin yanka ba, har sai bayan wata hudu tukunna Allah ya hore mashi, shin yankannan tana kanshi ko ta fadi???

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

Ya tabbata a cikin hadisin Tirmizi cewa ana yiwa abin da aka Haifa Akika ranar 7/wata.

Wasu  malaman daga cikin Sahabai da wadanda suka zo bayansu sun yi karin bayani cewa: in ba'a samu damar yi ba ranar bakwai ana iya  yi ranar 14 ko kuma  ranar 21.

Duk wanda bai samu damar yiwa dansa Akika  ba a  kwanakin da aka ambata a sama,  to babu wani kayyadajjen lokaci, zai iya  yi duk lokacin da ya samu dama.

AKIKA hakki ne akan Uba zai yi kyau ya yiwa dansa a lokacin da Annabi S. a. w  ya ambata, in kuma ba shi da dama, ya yi masa da zarar Damar ta samu.

Allah ne mafi sani

Don neman karin bayani duba: Daka'iku Ulin Nuha 1/615.

 

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

26/08/2017


No comments: