GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Monday 23 December 2013

TAMBAYA TA DARI BIYU DA SITTIN DA DAYA (261) ZUWA TA DARI BIYU DA TAMANIN (280)

261. TAMBAYA

INA YAWAN FITAR DA MANIYYI, SABODA Mijina  BA LAFIYA?

 

Assalamu Alaikum, Dr macece mijinta

ba yada lafiyan aure tsawon lokachi, sai ya

zamana tana yawan releasing ba sai tayi wani

dogon tunani na sha’awaba, ya matsayin

ibadarta yake ?

Amsa

Wa'alaikumus salam.

To gaskiya abin da yake dai-dai shi ne :

 ya nemi magani, in kuma bai samu ba, ana iya raba auran, tun da yana daga cikin manufofin aure, kadange ma’aurata daga fadawa haramun, kamar yadda shararren hadisinnan ya tabbatar. Yawan fitar maniyyi zai iya zama lalurar da za ta iya haifar da saukin sharia, saidai na ki ba zai zama lalura ba, saboda iyayenki za su iya wajabtawa mijin neman magani, in kuma bai samu ba, za ku iya rabuwa, Allah ya azurta kowa dağa falalarsa.

Cigaba da zamanku a wannan halin yana iya jefa

ki cikin hadari, mata nawa ne suka zama mazinata ta hanyar wannan sababin ? ya wajaba ki yi wanka duk sanda maniyyin ya fita, tun da ya fita ne ta hanyar jin dadi.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

262. TAMBAYA

INA YAWAN FITAR DA MANIYYI, SABODA Mijina  BA LAFIYA?

 

Assalamu Alaikum, Dr macece mijinta ba yada lafiyan aure tsawon lokachi, sai ya zamana tana

yawan releasing ba sai tayi wani dogon tunani na sha’awaba, ya matsayin

ibadarta yake ?

 

Amsa

Wa'alaikumus salam.

To gaskiya abin da yake dai-dai shi ne :

 ya nemi magani, in kuma bai

samu ba, ana iya raba auran, tun da yana daga

cikin manufofin aure, kadange ma’aurata daga

fadawa haramun, kamar yadda shararren

hadisinnan ya tabbatar.

 

 Yawan fitar maniyyi zai

iya zama lalurar da za ta iya haifar da saukin

sharia, saidai na ki ba zai zama lalura ba,

saboda iyayenki za su iya wajabtawa mijin

neman magani, in kuma bai samu ba, za ku iya

rabuwa, Allah ya azurta kowa dağa falalarsa.

Cigaba da zamanku a wannan halin yana iya jefa

ki cikin hadari, mata nawa ne suka zama

mazinata ta hanyar wannan sababin ? ya

wajaba ki yi wanka duk sanda maniyyin ya fita,

tun da ya fita ne ta hanyar jin dadi.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

263. TAMBAYA

WANDA YAKE CIWON IDO, ALWALA ZA TA FADI A KANSA?

 

 Assalamu alaikum,malam Inada tambaya?

Idan mutum akayi masa aiki a ido ance kar ruwa ya taba, toh idan zai yi salla taimama zaiyi ko zai iya yin alwala ba tare da sa ruwa a wajen ba? Allah ya saka da alkhairi.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

zai yi alwala

cikakkiya, sai ya tsallake wurin da yake da ciwon, saboda Ka’idar : ﺍﻟﻤﻴﺴﻮﺭ ﻻ ﻳﺴﻘﻂ ﺑﺎﻟﻤﻌﺴﻮﺭ

Duk ibadar da za’a iya yin wani bangarenta, to

dukanta ba ya saraya, saboda rashin iya aikata

wani bangarenta, sai fa idan bangaren na ta,

shari’a ba ta bukatarsa, kamar mai olsar da zai

iya yin azumi zuwa azahar ya sare,

Allah ne mafi sani

21/12/2016

Dr. Jamilu Zarewa

 

264. TAMBAYA

HUKUNCIN DAGA HANNU A KOWACE KABBARA YAYIN SALLAN JANA'IZA

 

Assalamu alaikum wa rahmatullah, barkan mu da yaw da fatan an yi sallar juma'a lafia malamai ina neman qarin bayani Akan sallar janaza. Wai a dukkan kabbarorin sai an daga hannu ?ko ya abin yake بارك الله فيكم

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Bayan an daga a kabbara ta farko, toh  sauran kabbarorin ba sai an daga ba, in kuma an daga shima babu laifi

Wallahu A'alam.

Malam Nuraddeen Muhammad (Mujaheed)

15 /07/2017

 

265. TAMBAYA

ZAN IYA YIN AZUMIN SITTU SHAWWAL ALHALI INA MATAFIYI?

 

Assalam alaykum. Mallan Dan Allah a taimaka a answer min tambaya na. Nice nayi bulaguro kuma INA sallan kasaru, shin Dan Allah mallan zan Iya yin azumin sitta Shawwal?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

Azumin sitta shawwal nafila ne, tafiya bata hana yin ibada ta nafila shiyasa ma manzon Allah yakanyi sallar nafila akan abin hawan sa yayin da yake halin tafiya, tare da cewa Sallar farillar ma an yi rangwame ga matafiyi ya sallaci raka'a biyu don saukakawa gare shi, amma duk da haka baya hana manzon Allah yin nafila, don haka dai babu laifi kiyi idan bazaki wahala ba.

Wallahu A'alam.

Malam Nuraddeen Muhammad (Mujaheed)

16/07/2017

 

266. TAMBAYA

HALASCIN KARATUN AL-QUR'ANI ANA RUWAN SAMA

 

Asssalamu Alaikum, mallam shin yahalasta akaranta Al Qur'ani  yayinda ake ruwan sama.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam.

Babu wani nassi daya haramta karanta alkur'ani yayin saukar ruwan sama, tare da haka kada amanta da yin azkaar lokacin saukar ruwan sama kamar yadda yazo a sunna, ga addu'ar :-

 

اللهم صيبا نافعا

Ko

 اللهم اجعله صيبا نافعا

 

Wallahu A'alam

Malam Nuraddeen Muhammad (Mujaheed)

14/07/2017

 

267. TAMBAYA

HUKUNCIN TABA JIKIN MACE

 

Assalamu Alaikum Allah ya karawa Malam Lafiya Tamabaya ta itace menene hukuncin taba jikin mace Dan yaji dadi kuma ba matarsa bace har yakai ga ya fidda Mani.

 

AMSA

Wa'alaikium salam warahmatullah wabarkatuhu  saika je kayi wanka da istigfari idan ba matarka bace wallahu ta'ala a'a lam.

Allah shine mafi sani

Amsawa

Dr.ABDALLAH USMAN GADON KAYA

 

268. TAMBAYA

MIJINA BA YA SALLAH, KO ZAN IYA NEMAN YA SAKE NI?

 

Assalamu alaikum malam ya karatu, Allah ya kara basira, malam wata mata ce take son a fada mata hukuncin zama da mijinta da bai damu da sallah ba, ko da kuwa lokacin Ramdahana ne, sannan kuma yana tilasta mata ya sadu da ita a lokacin watan Ramdhana da rana, bayan haka yana saduwa da ita tana jinin  haila, kuma ta fada masa haramun ne amma ya ki ya daina,  shin malam za ta iya neman saki tun da ba ya bin dokokin Allah ko ta cigaba da zama da shi? , na gode Allah ya karawa malam basira da hazaka .

 

Amsa :

Wa alaikum assalam To 'yar'uwa  mutukar an yi masa nasiha bai bari ba, to za ki iya neman saki, saboda duk wanda ba ya sallah kafiri ne a zance mafi inganci, kamar yadda Annabi s.a.w. ya fada a  hadisin da  Muslim  ya rawaito mai lamba ta : 81.

Ga shi kuma aya : 10 a suratul Mumtahanah ta tabbatar da rashin halaccin musulma ga kafiri, kin ga cigaba da zamanku akwai matsala a addinan ce.

Allah ya hana saduwa da mace mai haila a suratul Bakara aya ta :  222, Saduwa da mace da rana a Ramadhana babban zunubi ne kamar yadda hadisin Bukhari mai lamba ta : 616 ya tabbatar da hakan.

Saidai  zunubin barin sallah shi kadai ya isa ya raba aure, idan har bai sake ki ba, za ki iya kai shi kotu, alkali ya raba ku.

Don neman Karin bayani duba Al-minhajj na Nawawy 2\69.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

6\3\2015

 

269. TAMBAYA

FURTA SAKI, AMMA MATARSA BA TA JI BA ?:                                                                       

Asslamau alaikum. Malam shin mutum ya furta saki ga matarsa ba ta jiba, shin ta saku? 

            

Amsa:                                                                  

 Wa alaikum assalam To dan'uwa matar ta saku, saboda sanin an sake ta, ba shi daga cikin sharudan saki, mutukar miji ya furta saki, mace ta saku koda ba ta ji ba,  yana daga cikin ka'idoji a wajan malaman fiqhun musulunci:

-Duk wanda ba'a damu da yardarsa ba wajan tabbatuwar abu, ba'a damuwa da saninsa, yardar mace ba sharadi ba ce wajan zartuwar saki,  haka ma saninta an yi sakın ba sharadi ba ne wajan tabbatuwarsa                                                             Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

 

270. TAMBAYA

NASAN YADDA AKE TAIMAMA

SHIN SALLAR NAFILA ITAMA ANA QABLI DA BA'ADI CIKIN TA

 

Dr tambaya ta itace yaya ake taimama sannan kuma sallar nafila kamar sallar asham shin itama anayi mata kabli da ba'adi kamar ydd ake yiwa sallar farilla ?

 

AMSA

Wassslam alaikum warahamatullah wabrakatuhu

To dan uwa dangane da yadda ake taimama shine mutum zai samu kasa mai tsarki ko wuri mai tsarki wanda yake da kasa a wajan kokuma kura sai mutum ya bude tafin hannayensa biyu ya shafi kasar sannan ya karkade, kasar daya debo ko tsakuwar, saiya shafi hannayensa biyu amma iya wuyan hannun sai

kuma ya shafa fuskarsa baki daya idan mutum yayi wanann ya aikata taimama ta sunnah sannan bugun kasar sau daya akeyi shine abinda hadisi ingantacce sahihi yace

Hadisin da yace ayi taimama bugu biyu bai inganta ba.

Dangane da bayani akan kabli ko ba'adi a sallar nafila babu shakka itama sallar nafila anayi mata kabli da ba'adi domin itama sallah ce

Allah shine mafi sani

Amsawa

Dr. Abdallah Gadon kaya

18/07/2017

 

271. TAMBAYA

ZAN SAKI MATATA SABODA TANA DA CUTAR AIDS?

                                                                                              

Assalamu alaikum. Malam matata ta yi rashin lafiya, da aka gwada ta, sai aka ce tana da cutar aids, ni kuma an gwada ni amma an ce bani da ita, Sannan an gwada ragowar matana, suma an samu ba su da ita, gaskiya malam ina so zan sake ta, saboda kar ta shafe mu, amma ina neman shawara ?

 

 Amsa                                                                                                                                     Wa alaikum assalamu To dan'uwa cutar aids tana daga cikin cututtuka sababbi, wadanda ba'a tattauna su ba a manyan kundayen musulunci, saidai  idan muka duba manufar da ta sa aka shar'anta saki wato tunkude cuta da matsala, daga daya daga cikin ma'aurata ko su duka, za muga ta tabbata a wannan cuta, tun da ilimin likitanci ya tabbatar da cewa cuta ce mai hadari kuma  ana daukarta, don haka ya halatta ka sake ta, saboda wannan dalilin tun da malaman Fiqhu sun halatta raba aure saboda cutar kuturta, kamar yadda hakan ya zo a Minahul Jalil Sharhu Muktasarul Khalil : 6\478   Cutar Sida kuma tafi kuturta tsanani.

Sannan ba za'a kalli cutuwar da za ta yi ba, bayan an saketa, domin yana daga cikin ka'idojin Sharia : kau da kai daga tunkude cutar da za ta shafi wani saboda cutar da za ta game,Cigaba da zama da ita zai jawo ka dauki cutar, kuma iyalanka su dauka, wannan yasa ba za'a waiga zuwa damuwarta ba a nan wurin.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

30/8/2015

 

272. TAMBAYA

HUKUNCIN MACE TA YI TAFIYA BA TARE DA MUHARRAMI BA

 

Mene ne hukuncin mace ta yi tafiya ba tare da Muharrami ba?.

 

AMSA:

An hana mace ta yi tafiya face tare da Muharrami wanda zai tsare ta kuma ya kare ta daga barnan mabarnata da fasikancin fasikai.

Hakika hadisai ingantattu sun zo wanda suke hana mace ta yi tafiya ba tare da Muharrami ba, daga cikin su:

An rawaito daga Abdullahi Dan Umar, Radhiyallahu Anhu, ya ce: Manzon Allah, Sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce: Kada mace ta yi tafiya na kwanaki uku face tare da ita akwai Muharrami.

Sannan an karbo daga Ibn Sa'id, Radhiyallahu Anhu, Lallai Manzon Allah, Sallallahu' alaihi wa sallama, Ya hana mace ta yi tafiya yini biyu ko darare biyu face tare da mijinta ko Muharraminta.

Kuma an karbo daga Abi Hurairah, Radhiyallahu Anhu, daga Manzon Allah, Sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce: Ba Ya halatta ga mace ta yi tafiya na jini da dare face tare da ita akwai Muharraminta. Bukhari da Muslim ne suka riwaito.

Amsawa:

Sheikh Saleh al-Fauzan, Rahimahullah

A duba littafin فتاوى المرأة المسلمة shafi na 863.

Tattarawa:Umar Shehu Zaria_

 

273. TAMBAYA

INA KOKWANTO KO NA FITAR DA ISKA; YA SALLATA?

 

Assalamu alaikum

Malam nicenakefama da lallurata basir Amman bayayawaitasani hutu sainazowurin alwala ko sallah sai ya ring a sakani konkonto kamar inafidda hutu to Malam menene hukuncin alwalata da kuma sallah ta pls?

 

Amsa

Wa alaikumus salam zaki cigaba da alwalar ki ne saifa in kin samu yakinin fitar hutu (iska) wato kinji sauti kenan ko kuma kinji wari, toh a wannan hali saiki sake alwala, amma shi mujarradin kokonto baya warware alwala duk da dai akwai malaman da suke fahimtar cewa kokwanto na walwale alwala, amma dai maganar farko tafi karfi.

Wallahu A'alam

Amsawa

Malam NURUDDEEN MUHAMMAD MUJAHEED

20/07/2017

 

274. TAMBAYA

HUKUNCIN MACE TA YI TAFIYA BA TARE DA MUHARRAMI BA

 

Mene ne hukuncin mace ta yi tafiya ba tare da Muharrami ba?.

 

AMSA:

An hana mace ta yi tafiya face tare da Muharrami wanda zai tsare ta kuma ya kare ta daga barnan mabarnata da fasikancin fasikai.

Hakika hadisai ingantattu sun zo wanda suke hana mace ta yi tafiya ba tare da Muharrami ba, daga cikin su:

An rawaito daga Abdullahi Dan Umar, Radhiyallahu Anhu, ya ce: Manzon Allah, Sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce: Kada mace ta yi tafiya na kwanaki uku face tare da ita akwai Muharrami.

Sannan an karbo daga Ibn Sa'id, Radhiyallahu Anhu, Lallai Manzon Allah, Sallallahu' alaihi wa sallama, Ya hana mace ta yi tafiya yini biyu ko darare biyu face tare da mijinta ko Muharraminta.

Kuma an karbo daga Abi Hurairah, Radhiyallahu Anhu, daga Manzon Allah, Sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce: Ba Ya halatta ga mace ta yi tafiya na jini da dare face tare da ita akwai Muharraminta. Bukhari da Muslim ne suka riwaito.

Amsawa:

Sheikh Saleh al-Fauzan, Rahimahullah

A duba littafin فتاوى المرأة المسلمة shafi na 863.

Tattarawa:Mal Umar Shehu Zaria

 

275. TAMBAYA

WAYE YA DACE YA YI MA MACE WANKAN GAWA?

 

Waye ya dace ya yi ma mace wanka idan ta mutu?, kuma shin ya halatta Mace kafira wanda ba Musulma ba ta yi mace Musulma wanka idan ta rasu?. Sannan da shigar da ita Kabari sharadi ne dole sai Makusantanta, ko kuwa kowane Musulmi zai iya shigar da ita kabari?. Akwai wasu mutane shin ya halatta a bar su, su shigar da mace kabarinta?.

 

AMSA:

Musantan mace su ne za su yi mata wanka kuma za a yi la'akari da wanda suka fi kusanci daga cikin wanda za su iya kyautata wankan. Kuma ya halatta a wakilta kowace mace wanda za ta iya kyautata wanke ta, koda kuwa ba makusanciyarta ba ce. Haka nan ya halatta miji ya wanke matan shi, ita ta wanke shi.

Dangane da Mace kafira ta wanke Musulma, wannan bai halatta ba, domin wanke mamaci ibada ce, kuma Ibadan wanda ba Musulmi ba, bata inganta.

Dangane da shigar da mace kabarinta, ya halatta wani daga cikin Musulmi ya shigar da ita koda ba makusancinta ba ne, matukar zai kyautata haka.

Amsawa:

 Al-Lajnatu al-Daa'imah Lil iftaa'i.

A duba littafin فتاوى المرأة المسلمة shafi na 441.

 Tattarawa: Umar Shehu Zaria

 

276. TAMBAYA

YA YA KAMATA NAYI DA RIBAR BANKIN DA NA AMSA?

 

Assalamu alaikum malam Menene ra'ayin malaman Sunna akan kudin da banki suke karawa mutane a cikin Saving account? Ya yakamata ayi amfani dasu? Allah ya karemu daga aikata kuskure.

 

Amsa

Wa alaikum assalam Farko dai ya haramta ga musulmi ya bude accout din da za'a  dinga saka masa kudin ruwa a ciki, saboda Allah ya haramta cin riba ya kuma yi shirin yaki da Wanda bai daina ci ba  à cikin aya ta 275 a Suratul  Bakara da ayoyin da suka zo  bayanta.

Annabi SAW ya la'anci  mai cin riba da wanda ya rubutata da wanda aka wakilta da wanda ya yi shaida akanta. Kamar yadda Tirmizi ya rawaito a  hadisi ingantacce.

Idan mutum ya amshi Interest din Banki to ya wajaba ya tuba ga  Allah da niyyar ba zai sake amsa  ba, tun da Allah ya Hana.

A zance mafi inganci zai iya amfani da  kudin wajan yin aikin da zai amfani jama'a kamar gina Asibitoci ko kwatar da ruwa zai wuce ko kuma hanyoyin da mutane za su bi su  wala, saidai ba shi da ladan wannan aikin da ya yi, saboda ba dukiyarsa ba ce.

 wannan ita ce maganar manyan malaman musulunci na wannan zamanin kamar Sheik Ibnu Bazz da sauransu.

Allah ne  mafi  sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

27/07/2017

 

277. TAMBAYA

TARAYYAN MAZA DA MATA YAYIN SALLAN JANAZA

 

Shin ya halatta Mace ta yi tarayya da Maza yayin sallan Janaza?

 

AMSA:

Abun da yake asali a dukkan ibada wanda Allah Ta'ala Ya shar'anta a littafinSa ko ManzonSa, Sallallahu 'alaihi wa sallama, Ya nusar da mu a cikin sunnoninsa, shi ne, tana game maza da mata, har sai idan an samu wani dalili da ya kebance maza ko mata.

 Kuma sallan janaza tana daga cikin ibadu wanda Allah da ManzonSa suka shar'anta, don haka tana game maza da mata. Sai dai sahun mata yayin sallan janaza yana kasancewa ne a bayan sahun Maza, kuma ya tabbata cewa Mata sun yi ma Manzon Allah, Sallallahu 'alaihi wa sallama, salla kamar yadda maza suka yi masa, sai dai basu zuwa makabarta domin rufe mamaci saboda Manzon Allah, Sallallahu' alaihi wa sallama, ya yi hani akan haka.

Amsawa: Al-Lajnatu al-Daa'imah Lil iftaa'i.

A duba littafin فتاوى المرأة المسلمة shafi na 443.

 Tattarawa: Mal Umar Shehu Zaria.

 

278. TAMBAYA

ZAN IYA SHAN MAGANIN TSAYAR DA HAILA SABODA AIKIN HAJJI?

 

Assalamu alaikum.

 Tambaya gare mu kamar haka: Ya halatta mace ta tsayar da jinin haila saboda hajj?

 

AMSA:

Wa'alaykumussalam,

 To, 'Yar uwa ya halatta, mutukar likita ya tabbatar miki ba zai cutar da ke ba, sai dai tsayawa a Dabi'ar da Allah ya halicce ki akai shi ya fi kyau, saboda shan magunguna irin wadannan yana birkita kwanakin al'ada, kamar yadda bincike ya tabbatar.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

21\12\2015

 

279. TAMBAYA

YA HALLATA NA YIWA  WANI DAWAFI?

 

Assalamu alaikum, Malam, yayata ta jidda ta ce in tambaye ka mene ne hukuncin yin dawafi ga wani, saboda mutane suna yawan bugowa suna cewa a musu dawafi,  kuma ta ce in gaya ma wai don Allah ka amsa a face book,  saboda ana bukatar sanin amsar.

 

AMSA:

To, 'Yar uwa, babu wani dalili ingantacce wanda yake inganta yiwa wani dawafi, sannan kuma ba a samu magabata na kwarai suna yi ba, ga shi kuma dawafi ibada ce, ita kuma ibada ba'a yin ta sai da dalili daga al-Qur' ani ko Sunna, amma dai ana iya yiwa wani addu'a lokacin da mutum yake yiwa kansa dawafi.

Akwai dalilai da yawa wadanda suke nuna ingancin yiwa wani Umara ko Hajji, sai dai ba a samu na dawafi a karan kansa ba.

Kiyasin dawafi akan Hajji da Umara ba zai yiwu ba, saboda dawafi tsantsar ibadar jiki ce, hajji da umara kuma ibadu ne da suka hada jiki da dukiya. Duk ibadar da ta hada jiki da dukiya, tana amsar wakilci, amma wacce ake yin ta da jiki kawai ba ta amsar wakilci kamar sallah.

Allah ne mafi sani.

Duba Fatawaa Nurun Aladdarb mai lamba ta: 87

Amsawa:

Dr Jamilu Yusuf Zarewa

7\12\2014.

 

280. TAMBAYA

SHIN YA HALLATA NA YIWA  WANI DAWAFI?

 

Assalamu alaikum, Malam, yayata ta jidda ta ce in tambaye ka mene ne hukuncin yin dawafi ga wani, saboda mutane suna yawan bugowa suna cewa a musu dawafi,  kuma ta ce in gaya ma wai don Allah ka amsa a face book,  saboda ana bukatar sanin amsar.

 

AMSA:

To, 'Yar uwa, babu wani dalili ingantacce wanda yake inganta yiwa wani dawafi, sannan kuma ba a samu magabata na kwarai suna yi ba, ga shi kuma dawafi ibada ce, ita kuma ibada ba'a yin ta sai da dalili daga al-Qur' ani ko Sunna, amma dai ana iya yiwa wani addu'a lokacin da mutum yake yiwa kansa dawafi.

Akwai dalilai da yawa wadanda suke nuna ingancin yiwa wani Umara ko Hajji, sai dai ba a samu na dawafi a karan kansa ba.

Kiyasin dawafi akan Hajji da Umara ba zai yiwu ba, saboda dawafi tsantsar ibadar jiki ce, hajji da umara kuma ibadu ne da suka hada jiki da dukiya. Duk ibadar da ta hada jiki da dukiya, tana amsar wakilci, amma wacce ake yin ta da jiki kawai ba ta amsar wakilci kamar sallah.

Allah ne mafi sani.

Duba Fatawaa Nurun Aladdarb mai lamba ta: 87

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

7\12\2014. 

No comments: