GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Saturday 23 July 2022

TAMBAYA TA DARI BIYU DA TAMANIN DA DAYA (281) ZUWA TA DARI UKU (300)

 

281. TAMBAYA

WANDA YA SAKI MATARSA A ZUCI BA TA SAKU  BA!

Assalamu Alaikum,

Don Allah Malam, idan mutum da dare ya qudurta zai saki matarsa zuwa safe, amma bai furta ba zuwa safiyar kuma sai ya canza shawara. Shin yaya matsayin auren yake?

Allah Ya taimaka.

AMSA:

Wa alaikumus assalam, Mutukar bai furta ba kuma bai rubuta ba to Ba ta saku ba, saboda Allah ba Ya kama Al'ummar Annabi Muhammad S. A. W.  da zancen zuci kamar yadda hadisi ingantacce ya tabbatar.

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

01/08/2017.

 

282. TAMBAYA

WANDA YA MUTU YANA SHAN TABA SIGARI, BAI TUBA BA?

 

Assalamu Alaykum, Ina fatan Dr yana Lafiya. Dan Allah mene ne Hukuncin Mai shan taba (sigari), har ya

mutu bai tuba ba?. Na gode.

 

 

Amsa:

Wa'alaikumus salaam wa rahmatullahi wa barakaatuhu, Dukkan wanda ya mutu yana shan taba (sigari) bai tuba ba, yana karkashin ikon Allah, in ya so ya gafarta masa, in ya so ya kama shi da zunubin shan tabar da ya yi, saboda shan taba haramun ne, saboda ta kunshi cuta, kuma duk abin da yake cuta ne tsantsa haramun ne, kamar yadda ayoyin Alqur'ani da hadisan manzon Allah suka tabbatar.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

11/05/2016

3/8/1437

 

283. TAMBAYA

HUKUNCIN YIN DAWAFI DA SAUKAR AL-QUR'ANI GA MAMACI

 

Wani lokaci na kan yi dawafi ga wani daga cikin makusantana ko Mahaifina ko Kakannina wanda suka rasu, mene ne hukuncin haka?, sannan mene ne hukuncin sauke musu al-Qur'ani?. Allah Ya saka muku da alheri.

AMSA:

Abu mafi dacewa shi ne barin wadannan abubuwa da ka ambata saboda babu wani dalili da ya yi nuni akan haka.

Sai dai shari'a ta baka dama ka yi sadaka ga wanda kake so daga cikin makusantanka da ma wanda ba su ba matukar Musulmai ne, da yi musu addu'a da yi musu Hajji da Umra.

Amma dangane da yi musu salla da dawafi ko karatun al-Qur'ani, abu mafi dacewa shi ne ka bar shi domin babu dalili akan yin haka. Hakika wasu daga cikin Malamai sun halatta haka ta hanyan qiyasi akan sadaka da addu'a, amma abu mafi gamewa shi ne kar ka yi (domin asalin kowace ibada tsayawa ake yi har sai an samu umurni daga Allah ko ManzonSa).

Ga Allah nake fatan dacewa.

Amsawa:

Abdulaziz Bn Baz, Rahimahullah

A duba littafin فتاوى المرأة المسلمة shafi na 451-452.

Tattarawa:

Umar Shehu Zaria

 

284. TAMBAYA

HUKUNCIN FADIN "BALAA" A KARSHEN SURATU ATTIN

 

Assalam alaikum warahmatallah Malam dafatan kana lafiya amin. Malam akwai addua da akeyi a yayin da aka karanta Suratin Tin a karshen surar wato "Balaa nahanu ala zalika laminash shahideen". Ya ingancin wannan addua yake? Wassalam Allah ya kara lafiya.

 

AMSA

Wa alaikum assalam, akwai hadisin da Abu-dawud ya rawaito mai lamba ta (887) wanda ya tabbatar dá hakan, saidai malaman hadisi sun raunana shi kamar Nawawy a cikin Al-majmu'ú 3/563.

Saidai wasu daga cikin malaman Malikiyya sun só fadin hakan in an karanta karshen Surar WATTIN, hakanan wasu a cikin  Hanabila.

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

04/08/2017

 

285. TAMBAYA

YAUSHE AKE YIWA YARO KACIYA?

 

Assalamu alaikum malam, ina tambaya ne akan yiwa yaro kaciya shekara nawa ya kamata ayi masa ?

 

Amsa

Wa'alaikum salam,

To malam babu wani hadisi ingantacce wanda ya kayyade wani lokaci da za'a yiwa  yaro kaciya, saidai malamai suna cewa: babbar manufar yin kaciya ita ce  katanguwa daga najasar da za ta iya makalewa a al'aura, wannan ya sa ya wajaba a yiwa yaro kaciya dab da balagarsa, saboda idan ya balaga shari'a za ta hau kan shi kuma tsarkinsa ba zai cika ba, in ba'a yi masa kaciyar ba, daga cikin ka'aidojin malamai shine duk abin da wajibi ba zai cika ba sai da shi, to shi ma ya zama wajibi, amma mustahabbi ne ayi masa, tun yana dan karami, saidai wasu malaman sun karhanta yin kaciya ranar 7 \ga haihuwa, saboda akwai kamanceceniya da yahudawa.

Allah ne mafi sani

Don neman karin bayani duba Fathul-bary 10/349

Dr. Jamilu Zarewa

18/11/2014

 

286. TAMBAYA

INA SON DALILI AKAN KACIYAR MATA

 

Assalamu alaikum, don Allah malam a taimaka min da amsar wannan tambayar, ko Qur'ani da hadisi sun yi Magana akan halarcin kaciyar mata, ko kuma wani daga cikin magabata na kwarai ya yi Magana akan haka? 

 

Amsa

Wa'alaikum salam,

To 'yar'uwa akwai hadisai da suka zo akan cewa: mustahabbi ne, yin kaciyar mata, saidai an yi sabani akan ingancinsu, wasu malaman sun raunana su, wasu kuma sun inganta su. Baihaki a Sunanu Assugrah a hadisi mai lamba ta: 3712, ya rawaito mustabbacin yin kaciyar mata daga Ibnu Abbas da sanadi mai kyau.

 Hadisin da Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta a lamba ta: 108, daga Nana A'isha tana cewa: 

"Idan kaciya ta hadu da kaciya, to wanka ya wajaba" 

na nuna cewa : al'ada ne yiwa mata kaciya a zamanin Annabi (S.A.W) Ibnu- Abi-zaid Al-kairawany ya ambata a Risala shafi na: 410, cewa: yin kaciyar mata mustahabbi ne. Don neman Karin bayani duba Al-mugni 1\101. 

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

12\5\2015

 

287. TAMBAYA

BABU BAMBANCI TSAKANIN WIWI DA GIYA A HARAMCI

 

Assalamu Alakum.

Malam ina da tambaya kamar haka,shin tabar wiwi tana daukan dukkanin hukunce hukuncen da suka hau kan giya (barasa)ko kuwa akwai banbanci.Dafatan zanga amsan wannan tambaya a Zauren Fiqhu.nagode.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 mutukar ta amsa sunanta na WIWI kuma tana bugarwa, tabbas za ta dauki dukkan hukunce-hukuncen giya na haramci.

Annabi s.a.w. yana cewa "Dukkan abin da yake sanya Maye giya NE,  kuma dukkan giya haramun ce" kamar yadda Nasa'i  ya rawaito a hadisi ingantacce,  wannan sai ya nuna haramcin shan WIWI da duk abin da yake sanya maye.

Allah ne mafi Sani.

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

05/08/2017

 

288. TAMBAYA

TA HAIHU KAFIN TA CIKA WATA BAKWAI DA AURE ?

 

Assalamu Alaikum. Malam yarinya ne aka aurar da ita batayi wata bakwai ba 7 ta haihu cikakkiyar yarinya yar wata tara (9) to malam meye hukuncin auren kuma ya hallaccin jaririyar a musulunci?

 

Amsa

Wa'alaikum salam,

In har an San tana da ciki aka yi auran wannan hukuncinsa a fili yake, kuma  auran bai inganta ba  a zance mafi inganci, amma in haihuwa ta yi Kafin ta cola wata bakwai, kuma ba'a santa da ciki ba to dansa ne, saboda ayar suratu Lukman da tá suratul Ahkafi sun nuna cewa ana iya haife ciki a watanni shida.

Auran dá  aka yi dá cikin shege ba tare da an sani ba  ya inganta, saidai ba  zá'à danganta cikin zuwa mijin ba, tunda ba shi ya yi ba.

In har ya san tana da ciki bayan sun yi aure  bai halatta ya take  ta ba har saí ta haihu,  saboda fadin Annabi s.a.w. "Duk wanda ya yi imani dá Allah da ranar Lahira to kar ya shayar da ruwansa ga shukar waninsa" kamar yadda Abu-dawud ya rawaito.

In ta haihu za su iya cigaba dá mu'amalarsu ta aure,  musamman in bai sani ba saí dá aka daura.

Allah ne  mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

07/08/2017

 

289. TAMBAYA

SHIRIN YIN AURE, SAI TSOHON MIJINA YA CE DAMA CAN YA YI MIN KOME?

 

Assalamu Alaikum.

Malam mijina ya sake ni bayan na kammala idda, saura kwana uku na yi aure sai ya zo ya ce dama ya yi min kome, amma bai sanar da ni ba ne, don Allah malam yana da hakki, ko kuma na kyale shi na yi aurena ?  saboda gaskiya ina son wancan, amma kuma ba na so na sabawa sharia ?

 

Amsa

Wa'alaikumsalam,

To 'yar'uwa tabbas miji yana da damar da zai yiwa matarsa kome  mutukar tana cikin idda, kamar yadda aya ta :228,  a suratul bakara take nuni zuwa hakan,  Amma mutukar   bai yi mata kome ba har ta kammala idda to ba shi da dama akan ta, amma zai iya shiga cikin manema.

Idan ya yi da'awar cewa ya yi mata kome tun tana idda, amma bai sanar mata ba ne sai bayan ta kammala idda, to ba za'a gasgata shi ba, sai ya kawo shaidu, wadanda za su tabbatar da faruwar hakan.

Yana daga cikin ka'idojin sharia toshe duk hanyar da za ta kai zuwa barna, idan aka bar abin a bude, wanda yake kin matarsa, zai iya mata mugunta, ta wannan hanyar, hakan yasa malamai suka ce sai ya kawo shaidu za'a gaskata shi, idan kuma bai kawo ba za ta iya zuwa ta yi auran ta.

Saidai wasu malaman suna cewa : idan har matar ta gaskata shi, to ya isa, ko da bai kawo shaidu ba.

Allah ne mafi sani.

Duba : Al-mabsud 2\23 da Mawahibul-jalil 5\408

Dr. Jamilu Zarewa

29/12/2014

 

290. TAMBAYA

MIJINA YA YI MIN KOME, BAYAN NA SHIGA JINI NA UKU ?

 

Assalamu Alaikum

 Malam inada tambaya danAllah.A fahimta ta idan aka saki mace saki daya iddarta tsarki uku ne dalili fadin Allah subhaanahu cikin suratul bakara aya 228. Sai nazo naji sharhin wani malami cewa"idan aka saki mace cikin tsarki zata kirga wannan tsarki a matsayin tsarki 1,idan tayi al'ada ya zama tsarki na 2 kenan idan ta sake al'ada tsarki uku kenan ma'ana ta gama iddarta. Ko kuma yace idan tana al'ada aka saketa to idan ta sake wata al'adar zata ce 1,ta kara wata tace 2,ta kara wata tace 3,ta gama iddarta kenan. Tambaya anan malam itace ,saboda fahimta ta ta tsarki uku,mun sami sabani da miki na har saki ya auku kuma ina cikin tsarki,nayi tsarki na daya,nayi na biyu ina cikin al'ada ta uku ya ce ya maidani kuma na koma. duba da sharhin malamin da na fada maka ina matsayin kome na a shari'a ?danAllah malam ina cikin fargabar ko mun sa6ama shari'a .idan ko mun sa6a malam mecece mafita? Allah ya karawa malam lafia da basira Amin.

 

Amsa

Wa'alaikummussalam,

'Yar'uwa in har kin shiga jini na uku, a iddarki, ta bayan saki sannan mijinki ya miki kome, to komen ya inganta a bisa mazhabar Abu Hanifa, amma a fatawar Imamu Malik kin kammala idda, tun da kın shiga cikin jini na uku, saidai duk mazhabar da kika dauka kika yi aiki da ita a nan wurin, ta yi, tun da lafazin Kur'i da ya zo a aya ta : 228 a suratul Bakara yana daukar ma'anar haila, yana kuma daukar ma'anar tsarki, Don haka in har kin tabbata kafin kammala jini na uku ya miki kome, to cigaba da mu'amalar auranku babu matsala.

 Allah ne mafi Sani.

Don neman Karin bayani duba: Tafsirin Ibnu Kathir 1\542.

Dr. Jamilu Zarewa

29/12/2014

 

291. TAMBAYA

MUTUM NE YA SIYO HATSI, BAYAN YA SIYO, SAI FARASHIN HATSIN YA TASHI, SHIN YA HALASTA YA QARA KUDIN KO KUWA ZAI SAYAR A YANDA YA SAYO?

 

Assalamu Alaikum warahamatullah

malam,mtum ne ke sana'a irin    su shinkafa,mai,wake da sauransu ,toh  sai ya siyo su a farashin da yake siyarwa,ana haka sai farashi ya hau, toh zai sayar a farashin daa ne kokuwa zai qara ne ya  cigaba da siyarwa?

Amsa

Wa alaikumus salam  Shari'ar musulunci ba ta qayyade ma dan kasuwa nawa zai sayar da kayansa na kasuwanci ba, sai dai Annabin rahama (SAW) ya yi addu'a ga dan kasuwa ya ce: "Allah yayi rahama ga dan kasuwan da zai saro da sauqi, ya sayar da sauqi"

A saboda haka; babu wata tanadaddiyar doka a shari'a da ta iyakance ma dan kasuwa yadda zai saida kayansa da ya saro, sai dai ya tausaya ba tare da ya cutar da kansa ba.

A kan haka; ya ga dama ya cigaba da saida tsohon akan farashin da, har ya qare, sannan ya tada farashin, ko kuma ya canza farashin kafin qarewar tsohon don in yaje sari yanzu zai sayo da tsada.

Imam Ibn Hazm ya fada a cikin"Almuhalla": *Ba  Wanda ke da ikon qayyade ma dan kasuwa yadda zai sa farashin kayansa; hatta gwamnati

Amma Shaikhul Islam Ibn Taymiyyah ya ce: *Idan gwamnati ta fahimci yan kasuwa na wasa da farashi;to ya halasta ta qayyade farashi

Wallahua'alam.

Amsawa

Malam Basheer Lawal Muhammad Zaria

07/08/2017

 

292. TAMBAYA

WANDA YA SAKI MATARSA ACIKIN MAYE, BA TA SAKU BA!

 

Assalamu alaikum malam, tambaya ce dani. Mijina ne yasake ni sau biyu, sai yasha abin maye  yace na zo nasameshi, nii kuma banzoba saboda bana son abin da yakesha na maye, shine yace idan banzoba a bakin aure na. Shin yaya auren mu? Allah ya saka da alheri.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Malamai sun yi sabani game da aukuwar sakin wanda yake cikin maye:

1. Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa idan ya  saki matarsa, tabbas sakin ya auku,  saboda shan giya sabon Allah né,  kuma shi ya jawowa kansa,  don haka ba za'à yi masa uzuri ba, wannan ita ce maganar Abu-hanifa da Malik  da Shafii a daya daga cikin zantukansa.

2. Sakinsa bai auku ba, saboda lokacin dá  Má'iz ya zo ya  tabbatarwa Annabi S. A. W. ya yi zina saidá ya tambaye shi ko ka sha giya né,  kamar yadda Baihaki ya rawaito a Sunanul-kubrah,  hakan saí ya nuna mashayin giya ba'a amsar maganarsa.

Sannan an rawaito daga sayyadina Usman da Ibnu Abbas cewa : sakin mashayin giya ba ya aukuwa, kuma  ba'a san wanda ya Sabá musu  ba  a cikin Sahabbai.

 wannan ita ce maganar Imamu Ahmad da Zahiriyya da Ibnu Taimiyya .

Babban Muftin Saudiyya na waccan lokacin Sheik Abdulaziz bn Bazz da wasu Malaman suna rinjayar da magana ta biyu  saboda mashayin giya bai san abin da yake fada ba,  hakan  sai ya sa ya yi kama da Mahaukaci wanda Alkalami ya saraya daga kan shi, kai har sallah ma an hana mashayin giya ya yi saboda ba ya cikin hayyacinsa,  kamar yadda aya ta (43) a Suratu Annisa'í  ta tabbatar  da hakan

Allah ne mafi sani.

Don neman karin bayani duba : Al-Mugni 7/289 dá kuma Sharhul Munti'i 10/233

Dr. Jamilu Zarewa

9/08/2017

 

293. TAMBAYA

YA HALATTA NA SAYI KARE SABODA GADI A GIDANA ?

 

Assalamu alaikum. Dr. Mene ne hukuncin ajiye kare a gida saboda gadi? Allah muke roko ya kara wa Dr lafiya da basira Ameen.

 

Amsa

Wa alaikum assalam, Ya tabbata a hadisin Bukhari da Muslim cewa:  "Mala'iku ba sa shiga gidan da yake akwai hoto ko KARE a ciki.

A wani hadisin mai lamba ta: 2974 da Muslim ya rawaito Annabi s.a.w. yana cewa: "Duk Wanda ya rike KARE, in ba Karen noma ba ko farauta ko kiwo, to Allah zai tauye masa  manyan lada guda biyu a kowacce rana.

Da yawa daga cikin malamai sun yi kiyasin KAREN GADI akan wadancan nau'ukan guda uku da suka gabata, don haka ya halatta musulmi ya riki Kare saboda gadi in har akwai bukatar hakan.

Ba ya halatta a siyar da kare kowanne iri ne, saboda Annabi S.a.w ya hana cin kudin Kare a hadisin da Muslim ya rawaito kuma ya kira Shi da dauda.

Duk da cewa an halatta wadancan nau'ukan guda hudu saboda bukata saidai bai halatta a siyar da su ba, saboda Ka'ida sananniya a wajan malaman Fiqhu wacce take cewa:

ما جوز للحاجة لا يجوز أخذ العوض عليه

Idan mutun yana bukatar daya daga cikin wadanchan nau'uka na karnuka guda huɗu da suke halatta, kuma bai samu wanda zai ba shi kyauta ba,  ya halatta ya siya, Amma zunubin sayarwar yana kan wanda ya sayar tun da shi ne bai bayar ba, kamar yadda Ibnu Hazm ya fada a littafinsa na Muhallah 4/793, Ka'ida tabbatacciya a wajan malamai tana cewa:

ما حرم سدا للذريعة يباح للحاجة أو المصلحة الراجحة

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

16/05/2017

 

294. TAMBAYA

TSAKANI KAFIRI DA MACE MUSULMA, WA  ZAN  ZABA ?

 

Assalamu Alaikum. Na karanta post din da kayi akan Shugabancin Mata, inda ka nuna bai halatta mace ta yi shugabanci ba in ba na gidanta ba, Ina so ka dan yi mana Karin bayani  idan aka samu takarar shugabanci tsakanin Kafiri  da kuma Mace Musulma, wanne ya kamata mutane su zaba a matsayin Shugaba?

 

Amsa

Wa'alaikum salam.

To dan'uwa amsa wannan tambayar yana da wahala, saboda ban ga littafin da ya tattauna mas'alar ba, amma dai na nemi taimakon  amsa tambayar wajan babban malaminmu Prof. Muhd Sa'ad Al-yuby, don haka ga abin da zan iya  cewa:

Farko dai zaben kafiri haramun ne, saboda fadin Allah madaukakin sarki "Kuma Allah bai sanya wata hanya ba ga kafirai akan muminai" Nisa'i aya ta : 141, hakan sai ya nuna bai halatta musulmai su sanya kafiri ya mulke su ba,   Kamar yadda zaben mace  a matsayin shugaba shi ma haramun ne saboda hadisin Abu-bakrah inda Annabi s.a.w. yake cewa ; "Duk mutanen da suka sanya mace ta zama shugabarsu, to ba za su rabauta ba"  kamar yadda Bukhari ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta: 4425, Ibnul-kayyim yana cewa: kore rabauta  dalili ne da yake nuna haramcin abu . Bada'i'ul-fawa'id  4\812.

Saidai kamar yadda malaman shari'a suke cewa: duk lokacin da abubuwa biyu  haramtattu suka hadu, ya zama  dole sai an aikata daya daga ciki, to sai a dauki wanda ya fi saukin haramci a aikata.

Idan muka kalli manufar shugabanci a musulunci, za mu ga ta kunshi : jagorancin mutane da kuma tsayar da addini, wannan manufar za  ta fi tabbatuwa idan aka zabi mace musulma, fiye da kafiri Crister.

Don haka mutukar matar tana da kokari wajan addini, to ita ya fi kamata a zaba, ba don kasancewar ya halatta a zabe ta ba, sai don kawai hakan ya fi saukin haramci, kuma babu yadda za'a yi sai a zauna babu shugaba.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamil Zarewa

22/01/2015

 

295. TAMBAYA

HUKUNCIN AUREN YAHUDU KO NASARA

 

Malam musulmi zai iya auren ahlul-kitab tana addininta yana musuluncinsa ?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam.

To dan'uwa Allah madaukaki ya halatta auren ahlul-kitabi, wato Yahudu ko Nasara, kamar yadda ya yi bayanin hakan a cikin suratul Ma'ida aya mai lamba ta:

(5), kuma an samu wasu daga cikin sahabai, sun aure su kamar Usman dan Affan - halifa na uku a musulunci- ya auri Banasariya, haka Dalhatu dan Ubaidillah ya auri Banasariya, sannan Shi ma Huzaifa ya auri Bayahudiya, Allah ya kara musu yarda. duba : Ahkamu-ahlizzimah 2\794.

Saidai malaman wannan zamanin suna cewa, abin dayafi shine rashin auren Ahlul-kitab saboda yadda zamani ya canza, domin da yawa idan mijinsu musulmi ya mutu yaran suna zama kirista, kai wani wani lokacin ko da sakinta ya yi zata iya guduwa da yaran, sannan zai yi wuya ka samu kamammu wadanda ba su taba zina ba a cikin su.

Wasu kasashen kuma idan za ka auri kirista daga cikinsu dole zai ka yarda da dokokin kasarsu, a lokuta da yawa kuma za ka samu dokokin sun sabawa ka'idojin musulunci .

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

02/12/2016

 

296. TAMBAYA

MACE, ZA TA IYA YIN AURAN KASHE WUTA !

 

Assalamu Alaikum,malam menene

hukuncin wadanda sukayi auran kisan wuta suka

maida aurensu, kuma menene hukuncin auren

nasu?

 

Amsa

Wa alaikum as salam,

 Auren kisan wuta bai halatta ba. Saboda Annabi (S.a.w) ya la’anci wanda ya yi da kuma wanda aka yi

saboda shi, kamar yadda Tirmizy ya rawaito

kuma ya inganta shi Idan miji ya yi aure da

niyyar halattawa mijin baya, auran batacce ne,

amma idan mace ce ta yı da wannan niyyar,

kuma mijin da ta aura bai sani ba, to auran ya

yi.

Saboda ba dole ba ne mijin ya sake ta. Yana

daga cikin Ka’idojin sharia:

 ﻣﻦ ﻻ ﻓﺮﻗﺔ ﺑﻴﺪﻩ ﻻ ﺃﺛﺮ

ﻓﻲ ﻧﻴﺘﻪ

 Duk wanda babu saki a hannunsa, to

niyyarsa ba ta da tasiri.

 Allah ne mafi sani 

Dr. Jamilu Zarewa

27/12/2016

 

297. TAMBAYA

YAYI WA MATARSA ZIHARI SAI YA SAKE TA KAFIN YAYI KAFFARA

 

Assalamu Alaikum, Malam ina da tambaya? Namiji ne ya yi wa matarsa zihari, maimakon ya yi kaffara sai ya sake ta, ya sake wani auren. Malam ya matsayin wannan sakin da matsayin auren?.

Allah ya bada ikon isar da wannan sako ga  Malam.

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 Auransa na biyun ya inganta saboda ba su da alaka da juna.

Wasu Malaman sun tafi akan cewa mutukar saki uku ne, to wancan ziharin ya warware, amma in saki daya ne kuma ya yi kome, to bai halatta ya taba ta har sai ya yi kaffarar ziharin, kamar yadda Ibnu Khudaamah ya fada a cikin Al-Mugni.

Allah ne mafi sani.

Amsawa

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

01/06/2017

 

298. TAMBAYA

HUKUNCIN DILLANCIN AURE

 

Assalamu Alaikum,

 Malam menene hukuncin 'yan matan da suke bada hotunansu ga tsofafi don su nema musu mijin aure ?

 

AMSA

Wa'alaykumussalam,

Addinin musulunci ya haramta kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, amma ya halatta ka kalli mace, idan kana so ka aure ta, kamar yadda ya zo a cikin hadisi, inda Annabi s.a.w. yake cewa : "Idan dayanku yana neman aure, to in ya sami damar kallon abin da zai kira shi zuwa aurenta, to ya aikata hakan" ABU DAWUD Malamai sun yi sabani akan wurin da ya kamata mutum ya kalla a jikin mace lokacin da yaje neman aure :

*1*. Akwai wadanda suka ce zai kalli fuska da tafin hannu ne kawai.

 

*2*. Wasu malaman sun tafi akan cewa : zai kalleta a kayan da take sawa a cikin gida, ta fuskace shi ya kalle ta, sannan ta juya baya ya kalleta. Wannan ra'ayin shi ne ya fi dacewa, saboda ta haka mutum zai san yanayin matar da zai aura. Ta hanyar bayanan da suka gabata, za mu iya fahimtar cewa aikin dalilin aure ya hallata, amma da sharuda, ga wasu daga ciki :

*1*. Ya zama hoton ya fito da asalin fuskar matar, bai KWARZANTA ta ba, ta yadda za'a iya yaudarar namijin, ko a rude shi.

*2*. Ya zama wacce za'a bawa hoton mai amana ce, ta yadda ba za ta nunawa wanda ba shi da nufin aure ba, saboda asali ya haramta ayi kallo zuwa ga matar da ba muharrama ba, sai in akwai lalura, sai ga wanda yake nufin aurarta, wannnan yana nuna cewa, bai halatta asa irin wannan hoton na neman aure ba , a face book, ko a jarida.

*3*. Ka da hoton ya kun shi fito da tsaraici, ya wajaba a tsaya a iya inda shari'a ta bada umarni.

*4*. Zai fi dacewa ace mace ce za ta yi dalilin aure, saboda in namiji ne, zai iya fitinuwa da hotunan da yake gani, sai barna ta auku, don haka ita ma macen ya wajaba ta ji tsoron Allah a cikin aikinta.

Allah shi ne mafi sani

   Amsawa

Dr. jamilu zarewa

22/11/2016

 

299. TAMBAYA

HUKUNCIN JININ BARI

 

 Assalamualaikum, malam ina da tambaya, Dan Allah idan

mace ta yi barin ciki na wata biyu wannan jinin

ya zaka na ciwo ko zata daina azumi sallah

 

Amsa

Wa'alaykumussalam,

To dan’uwa wannan jini ba zai hana

sallah da azumi ba, saboda ba jinin haihuwa bane,

malamai suna cewa : duk cikin da ya zube

kafin halittar mutum ta bayyana, to ba zai hana

sallah da azumi ba, halittar mutum tana bayyana ne daga 80-90 daga samuwar ciki, saboda haka

duk cikin daya zube kafin haka, to jininsa ba

zai hana sallah ba, ba zai hana azumi ba, amma

mutukar an busawa yaro rai ko kuma halittarsa

ta fara bayyana, to za’a bar sallah da azumi.

Allah ne mafi sani.

30/11/2016

Dr. Jamilu Zarewa

 

300. TAMBAYA

ALAMOMIN KARBAR TUBA

 

Assalamu alaikum dan Allah malam akwai hanyar da mutum yake gane Allah ya yafe masa zunubin da yayi, ya kuma nemi yafiya ?

 

Amsa :

Wa alaikum assalam To dan'uwa akwai alamomin da malamai suka fada, wadanda suke nuna Allah ya karbi tuban bawansa, ga wasu daga ciki

*1.* Aikata ayyukan alkairi, da son yin abin da zai kusantar da shi zuwa ga Allah.

*2.* Mutum ya dinga kallon gazawarsa wajan biyayya ga Allah.

*3.* Ya zama yana yawan girmama zunubin da ya tuba daga shi, yana kuma jin tsoron komawa zuwa gare shi .

*4.* Ya dinga kallon dacewar da aka ba shi ta tuba, a matsayin ni'ima daga Allah.

*5.* Ya zama yana yawan nisantar zunubai, sama da kafin ya tuba.

*6.* Yawan istigfari.

*7.* Son kusantar salihan bayi.

Allah ne ma fi sani .

Amsawa

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA                                                   5/6/2014

No comments: