GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.TAMBAYADAAMSA.BLOGSPOT.COM

WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA FATAWOHI DA AMSOSHIN SU WADAN DA AKA YIWA WASU DAGA CIKIN MALAMAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI;{tambayadaamsa@gmail.com]

Tuesday 18 October 2011

TAMBAYA TA ASHIRIN DA DAYA (21) ZUWA TA ARBA'IN (40)


21. TAMBAYA

HUKUNCIN MUTUMIN DA YAKE TAKE WANDONSA

 

Assalamu alaikum,

Mene ne hukuncin mutumin da yake take wandonsa, shin ya halatta a bi shi salla?

 

AMSA

Take wanda a Musulunci haramun ne domin hadisai masu yawa sun zo suna hani akan haka, kuma ba lallai sai wando ba.

 

Manzon Allah, sallallahu 'alaihi wa sallama, ya ce:

 

 *"مَا أَسْفَلَ مِنْ الْكَعْبَيْنِ مِنْ الْإِزَارِ فَفِي النَّارِ"* رواه البخاري (5787).

 

Duk abun da ya wuce idon sawu (na tufafi),

to yana wuta. Bukhari ne ya ruwaito hadisi na 5787.

 

Malamai suka ce tun da har Allah Ta'ala Ya yi barazana da wuta, to wannan ya nuna babban laifi ne.

 

Dangane da batun bin shi salla matukar babu najasa a jikin tufan shi za a bi shi salla, domin laifin mai laifi bai hana a karɓa sallansa matukar ya yi ta yanda shari'a ta koyar kamar yadda Abdullahi Bn Umar ya yi salla a bayan Hajjaj Bn Yusuf al-Thaqafee.

 

Wallahu A'alam.

 

Amsawa:

Sheikh muhammad bello Al-adamawiy, Rahimahullah

 

22. TAMBAYA

HUKUNCIN KALLON  WASAN KWAIKWAYON ANNABAWA

 

Assalamu Alaikum

Malam Don Allah Tambaya Na ke da shi Da Fatan Za'a  Fahimtar da ni. -wai Shin Kaset din da akeyi na Tarihin Annabawa Ya Halatta A Kalle shi ? Allah Ya Saka Da Alkhairi .

 

Amsa

Wa'alaykumussalam.

 

To dan'uwa  malamai da yawa sun haramta yin wasan kwaikwayon annabawa saboda dalilai kamar haka :

 

1. Hakan zai iya bude kofar da wasu masu kallon za su yi  isgilanci ko ba'a ga annabawan Allah, isgilanci ga annabawa kuma yana iya  fitar da mutum daga musulunci, kamar yadda aya ta : 65 a suratu Atttauba ta yi nuni zuwa hakan.

 

2. Wasu daga cikin masu shirya film din suna wuce gona-da-iri, kamar masu nuna annabi Isa a matsayin Allah, addinin musulunci kuma ya haramta duk abin da zai kai a riki wani annabi ko managarci a matsayin Allah.

 

3. Irin wadannan wasannin na kwaikwayo, suna ragewa annabawa matsayi, saboda masu film din suna cakuduwa da matan da ba muharramansu ba, wanda hakan kuma  ragewa annabawa kima ne.

 

4. Kasancewar hakan ya sabawa hikimar Allah ta sanya shaidanu ba sa iya kama da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , kamar yadda ya zo a hadisi.

 

5. Kasancewar hakan zai jawo aki girmama annabawa, a kuma yi musu karya, domin wasu masu yin wadannan fina-finan mutanen banza ne, ka ga sai a dinga kallon annabawan da siffar wadannan.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

13/6/2014

 

23. TAMBAYA

MAHAIFIYATA TANA ZUWA WAJAN BOKA, INA NEMAN SHAWARA?

 

Assalamu alaikum

Dan Allah malam a fitar dani cikin duhu game da abin da yake damuna Mahaifiya ta ce ta je gurin malami ai mata naganin ciwon mara dz yake damunta, tace tana da ciki yakai shekara, amma likitoci sun yi scanning sunce ba komai to sai malamin ya ce mata asiri aka yi mata, kuma zai yi mata magani nan take ta haife abinda yake cikinta amma za ta kawo tunkiya da dubu bakwai, sai take min magana in kawo kudi a sayi tunkiyar kuma akai masa dubu bakwan, to gaskiya malam zuciyata ba ta aminta da malaman ba ne shi yasa ! Na keso ka bani fatawa shin irin wannan hanyar ta magani ta halatta a addini? Idan bata halatta ba wacce hanya zan bi wajen qin biyan kudin da kuma sanar da ita, saboda ina da matsala , ta bangaren aqeeda mun banbanta? Wassalam na gode malam Allah ya qara basira.

 

Amsa :

 

Wa alaikum assalamu To 'yar'uwa tabbas ba a warware sihiri ta hanyar sihiri, saidai ana iya warware sihiri ta hanyar ayoyin Alqur'ani, wasu malaman sun yi bayani cewa : ana iya warware sihiri ta hanyar karanta Ayatul-kursiyyu da Kuliya da Iklas da Falaki da Nasi, da kuma aya ta : 117 zuwa ta 122, na suratul A'araf, sai kuma aya ta : 79-81 a suratu Yunus, sannan sai a hada da aya ta : 65-70 a suratu Dhaha, za'a karanta su, sai a tofa a ruwan da aka zuba magarya guda bakwai.

Amma bai halatta ki taimaka mata ba, wajan bada wadannan kayan da boka ya nema, saboda ba'a yiwa iyaye biyayya a wajen sabon Allah.

Ya wajaba ki yi mata nasiha cikin hikima, ki sanar da ita cewa : Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa :" "Duk wanda ya je wajan boka, ya tambaye shi wani abu, Allah ba zai amshi sallarsa ba, ta kawana arba'in" kamar yadda muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 2230. Kin ga in mutum ya mutu a wadannan kwanaki akwai matsala, musamman ma tun da akwai hanyar da shari'a ta yarda da ita, a wani hadisin kuma yana cewa : "Duk wanda ya je wajan boka ya gaskata abin da ya fada, to tabbas ya kafurce da abin da annabi Muhammad ya zo da shi" kamar yadda ya zo a Sunanu-abi-dawud hadisi mai lamba ta : 3904, kuma Albani ya inganta shi .

INA GANIN DA IRIN WADANNAN HADISAN ZA KI IYA GANAR DA ITA, TA DAWO KAN HANYA.

 

Allah ne mafi sani.

Amsaw:

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

8\3\2015

 

24. TAMBAYA

NA SAKI MATATA SAU BIYU, SAI NA SAKE SAKINTA BAYAN DAURA  SABON AURE, KO AKWAI DAMAR KOME ?

Assalamu alaikum

Don Allah malam ka warware mana wannan matsala, yanzu haka muke cikinta, mutum ne ya sake matarsa shika Daya 1, ya koma da ita bayan wasu shekaru ya sake mata shika daya, har idarta ya kare ya sake biyan sadaki ya dawo da ita yanzu kuma sun sake rabuwa shika daya 1, kuma suna son junansu akwai aure a tsakaninsu ko sai ta sake auren wani ? shikan bayan da ya mata har idarta ya kare aka sake daura aure a matsayin shika nawa ne yake kanta nagode Allah ya kara imani da basira sai naji daga gareka

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To dan'uwa idan abin haka yake kamar yadda ka siffanta, to babu damar kome, sai in  ta auri wani mijin na daban, saboda igiyoyin da suke tsakaninku sun yanke gaba dayansu .

Auren da kuka sake, ba zai goge sakin da ka yi a baya ba, da ace ta auri wani bayan saki biyun da ka mata, kafin ka sake auranta, da ba'a kirga da saki biyun baya ba, a daya daga cikin maganganun malamai, amma tun da ba ta auri wani  ba, ya wajaba ku hakurewa juna .

Don neman Karin bayani duba : Al-mugni na Ibnu-Khudaamah 7\388 .

 

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

3\5\2015

 

25. TAMBAYA

AL'ADATA  TA RIKICE, SABODA SHAN MAGANIN TSARA IYALI ?

Assalamu Alaikum

Malam don Allah ina da tambaya, don Allah a taimaka min da amsa don kokarin gyara wa Akan lokaci. Malam matsala ta haihuwa greni duk haihuwa ta sai anyi min cs, sai likita ya bani shawarar tsarin iyali don in huta, sai daga nan al'adata Tarikice sai yazo yau bazan sake ganin Shiba sai bayan kwana biyar sai yazo min dayawa, to ni dai wanka na nkeyi nacigaba da ibadata to malam ibadata tayi ko da gyara. Sai kuma da watan Ramadan yazo min dana Kai iya kwankin da yake min wato kwana biyar sai nayi wanka nacigaba da azumi na kuma jinin yana zuwa bai dauke, don sai da yamin wajen kwana goma sannan ya dauke nayi wanka, to shine akace min sai na Rama wannan kwana ki goman shima. To malam ya azumin tawa take.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To 'yar'uwa Allah madaukakin sarki a cikin alqur'ani ya rataya hukuncin jinin haila ne da samuwarsa, don haka mutukar kin ga jinin haila da siffofinsa (Baki, ko karni) to ya wajaba ki bar  sallah da azumi, har zuwa lokacin da zai dauke, saidai in ya zarce iyaka ta yadda zai zama, yana zubo miki a mafi yawan kwanakin rayuwarki ko dukanta, to a lokacin ne yake zama jinin cuta ta yadda  ba zai hana sallah da azumi ba.

Duk da cewa tsara iyali ya halatta saboda hadisin Jabir wanda yake cewa "Mun kasance muna yin azalo (zubar da maniyyi a waje yayin saduwa) a lokacin da Qur'ani yake sauka, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 4911, saidai  yawancin magungunan tsara iyali suna birkita al'ada, wannan yasa barin su shi ne ya fi, in ba likita ne ya tabbatar da lalurar shan ba, ko kuma aka gane maganin ba ya crycutarwa ta hanyar jarrabawa.

 

Allah ne mafi sa ni

Amsawa:

DR. Jamilu Yusuf Zarewa

22\1\2016

 

26. TAMBAYA

WANDA YA TUBA DAGA ZINA SABODA HIV, ALLAH ZAI AMSHI TUBANSA !

 

Assalamu Alaikum

Malan, mutumen dayake mazinacine amasa wa'azi amma yaki yadaina...... Harsai da aka tabbatarmasa dacewa cutar HIV takamashi sannan ya tuba... To Allah gafarta malan miye matsayin wannan tubar tasa?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

 

In har ya tuba tuba ingantacce, Allah zai iya amsar tubansa.

Annabi S.a.w. yana cewa: "Allah yana amsar tuban bawa mutukar bai zo gargarar mutuwa ba", a wani hadisin kuma yana cewa "Duk wanda ya tuba kafin rana ta fito daga yamma Allah zai amshi tubansa".

Kasancewar ya samu cutar HIV ya daina ba zai hana a amshi tubansa ba, tun da akwai wadanda suna da cutar amma suna yi, tun da cutar ba ta hana jindadin zinar kwata-kwata.

Wanda ya bar zunubi saboda gajiyawa za'a rubuta masa alhakinsa cikakke, kamar yadda hadisi ingantacce ya nuni zuwa hakan.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

29/10/2017

 

27. TAMBAYA

YAWO BABU DAN-KWALI A TSAKAR GIDA ?

 

Assalamu alaikum, Allah gafarta malam shin zan iya yawo acikin gida ba dan kwali?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

 

Mace zata iya yawo babu Dan kwali idan tana tsakanin 'yan uwanta mata musulmai saboda al'aurar mace ga 'yar uwarta mace musulma tana kasancewa ne tsakanin guiwa zuwa cibiya, mutukar akwai mazan da ba muharramai ba to bai halatta ta bude kanta ba, saboda dukkan mace Al'ura ce in ban da fuska da tafukan hannu.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

24/1/2016

 

28. TAMBAYA

YADDA AKE ZAKKAR SHANU?

 

Assalamu alaikum

 Malam. mutum ne yake da shanu guda (168) yaya

zakkarsu za ta kasance ?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To Dan'uwa zakkar shanu, tana da mutukar sauki, saboda

duk guda talatin za ka fitar da wanda ya cika

shekara daya, duk kuma guda arba’in za ka fitar

da wanda ya cika shekaru biyu, kamar yadda

hakan ya tabbata a hadisin Mu’az wanda Abu-

dawud ya rawaito a Sunan a hadisi mai lamba

ta: 1576, kuma Albani ya inganta. Don haka

kana da zabi ko dai ka bayar da wadanda suka

cika shekara biyu guda hudu, ko kuma ka bayar

da wadanda suka cika shekara daya guda hudu,

da wanda ya cika shekara biyu guda daya.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

15/12 /2016

 

29. TAMBAYA

MATAR DA TA GAYYATO JININ HAILA KAFIN LOKACINSA,  YAYA SALLARTA?

                                                                  Assalamu alaikum,

Mallam ina hukunchin macen da in mijinta ya fitine ta da jima'i take shan magani don jini yazo mata, Yaya hukuncin jinin yaya kuma maganar sallah, ? tunda gayyato jinin ta yi.     

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

 

To 'yar'uwa Allah da manzonsa sun rataya hukunce-hukuncen jinin haila ne da samuwarsa, kamar yadda aya ta : 222 a suratul-Bakara take nuni zuwa hakan, duk da cewa gayyato shi ta yi  saidai zai dauki dukkan Hukunce-hukuncen haila, mutukar ya zo da siffofinsa.                                                       Gayyato jini saboda hana miji jin dadi bai dace ba, saboda duk dabarar da za ta kai zuwa haramun to ita ma ta zama sabon Allah, Ya wajaba ga mace ta baiwa miji kanta duk lokacin da yake bukata, in ba tana da uzurin da sharia ta yarda da shi ba,  don haka bai kamata mace ta hana mijinta saduwa da ita ba ta hanyar dabara.

              

 Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Zarewa

 31/10/2015

                                  

30. TAMBAYA

SANYA HAKORIN MAKKA A MA'AUNIN SHARIA ?

 

Assalamu Alaikum

Dr. dafatar ka tashi lafiya Alagafarta malam ina neman karin bayani game da Hauren makka da alhazzai suke sakawa akan cewa shima yana haddasa lum'a a lokacin da mutum ya zo kuskurar baki ruwa ba za su taba ainihin Hauren da Allah ya halicci mutum da shi ba?

 

Amsa

Wa alaikum assalam,

a zahiri sanya Haure bayan aikin hajji ba matsala ba ne ta fuskar Lam'a tun da kurkure baki sunna ne a wajan da yawa daga  malamai, wannan yasa rashin shafar ruwan ga hakori daya ba zai yi tasiri ba.

Amma zai iya zama matsala saboda yana iya janyo riya, tun da galibi wanda zai sanya yana yi ne saboda yaje hajji ko dan ace masa Alhaji, hakan ya sa barinsa shi ne ya fi.

 

Idan ya kasance an yi hauren ne da zinare to haramun ne namiji ya sanya saboda Annabi S.A.W. ya ce: (An haramta zinare ga mazajen Al'umata, amma an halatta ga matayansu)

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

1/11/2017

        

31. TAMBAYA

ZAN SAKI MATATA SABODA TANA DA CUTAR AIDS ?

 

Assalamu alaikum.

Malam matata ta yi rashin lafiya, da aka gwada ta, sai aka ce tana da cutar aids, ni kuma an gwada ni amma an ce bani da ita, Sannan an gwada ragowar matana, suma an samu ba su da ita, gaskiya malam ina so zan sake ta, saboda kar ta shafe mu, amma ina neman shawara ?

Amsa

                                                                                                                                        Wa alaikum assalamu To dan'uwa cutar aids tana daga cikin cututtuka sababbi, wadanda ba'a tattauna su ba a manyan kundayen musulunci, saidai  idan muka duba manufar da ta sa aka shar'anta saki wato tunkude cuta da matsala, daga daya daga cikin ma'aurata ko su duka, za muga ta tabbata a wannan cuta, tun da ilimin likitanci ya tabbatar da cewa cuta ce mai hadari kuma  ana daukarta, don haka ya halatta ka sake ta, saboda wannan dalilin tun da malaman Fiqhu sun halatta raba aure saboda cutar kuturta, kamar yadda hakan ya zo a Minahul Jalil Sharhu Muktasarul Khalil : 6\478   Cutar Sida kuma tafi kuturta tsanani.

Sannan ba za'a kalli cutuwar da za ta yi ba, bayan an saketa, domin yana daga cikin ka'idojin Sharia : kau da kai daga tunkude cutar da za ta shafi wani saboda cutar da za ta game,Cigaba da zama da ita zai jawo ka dauki cutar, kuma iyalanka su dauka, wannan yasa ba za'a waiga zuwa damuwarta ba a nan wurin.

 

Allah ne mafi sani

 

Amsawa:

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

30/8/2015

 

32. TAMBAYA

MAI TAKABA, ZA TA IYA FITA AIKIN GWAMNATI

 

Assalamu alaikum malam inada tambaya mace ce mijnta ya rasu kuma takasance tana aikin gomnati shin zata iya fita a lokacin da take takaba?

 

Amsa

Wa'alaiku mussalam

warahmatullah, a zahirin maganar malamai, mai takaba ba za ta je aikin gwamnati ba, tun da bai halatta mai takaba ta fita ba sai lokacin tsananin lalura, aikin gwamnati ba ko yaushe zai zama lalura ba, tun za'a iya ba ta hutu, in har ta nema, in tana da yadda zata cı abinci ya wajaba ta amshi hutu, ko da babu albashi. Saboda bin sharia shi ne zaman lafiya, duk wanda ya kiyaye Allah, to shi ma zai kiyaye shi, duk wanda ya yi hakuri Allah hakurkurtar da shi.

Amma idan ta rasa yadda zatayi ta cı abinci sai ta hanyar aikinta, to ya halatta ta yi da rana kawai, saboda Annabi (S.A.W) ya halattawa matan shahidai a zamaninsa, zama a gidan daya dağa cikinsu domin hira da debe kewa da rana, lokacin da suka takuru da zaman kadaici, duk da ya wajabta musu komawa gidansu in dare ya yi, Kamar yadda Baihaki ya rawaito, wannan sai ya nuna lalura tana halattawa mai takaba fita da rana, kamar yadda Ibnu-khudaama ya ambata a littafinsa na Mugni 8/130.

Duk da cewa wasu malaman Hadisin sun raunana hadisin Baihaki da ya gabata, saidai an samu  kwatankwacinsa daga maganar Abdullahi dan Mas'ud da Abdullahi dan Umar, Allah ya kara musu yarda, maganar Sahabi hujja ce, in har ba'a samu wani sahabin  ya saba maşa ba, kamar yadda yake a ilimin Usulul-fiqh.

 

ALLAH NE MAFI SANI

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

22/3/2016

 

33. TAMBAYA

AKWAI GADO GA DAN DA MACE TA SHAYAR DA IYAYEN SHI ?

 

Assalamu alaikum malamaina don Allah ga wata tambaya kamar haka : idan aka haifi yaro sai daga baya aka samu cewa da babanshi da mamarshi duk mace guda ta shayar dasu to wai wannan yaron yana da gadansu koko?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam.

 A na gado da takaba a auren da a ka gano rashin ingancinsa, kuma a na danganta yaro ga mahaifinsa. [AL-MUGNY; 8/590]

 

Wallahu A'alam.

Amsawa:

MALAM: NURUDDEEN MUHAMMAD (MUJAHEED)

25/10/2017

 

34. TAMBAYA

A GUJI MUGUWAR ADDU’A GA IYALAI!

 

As-salaamu alaykum Malam Allah ya

kara maka imani da fahimta Tambayata itace

Mahaifinane yake nuna banbanci a tsakanin mu

sannan yana yawan zagin mahaifiyata

musamman in ‘kanne na sunyi masa laifi sai ya

kama zaginta Sai na nuna masa rashin jindadina

da wannan Al’amari har ya kai ga mun daga ma

juna murya. Karshe sai ya fara yimin Allah ya

isa yana tsine mun.

Amsa

Wa'alaykumussalam

Ya wajaba uba ya yi adalci a tsakanin ‘ya’yansa, Annabi S.a.w. yana cewa : “Ku ji tsoron Allah ku yi adalci a tsakanin

‘ya’ya yanku” Wannan ya sa lokacin da Sahabi

Bashir ya yiwa dansa kyauta, ya nemi Annabi s

a w. ya yi shaida akan haka, ya tambaye shi :

shin Duka ‘ya’yanka ka yi musu kyauta ? sai ya

ce A’a, sai manzon Allah ya ce : Ba ka so su

zama daidai wajan yi maka biyayya ? ba zan yi

shaida akan zalunci ba”. Bukhari da Muslim sun

rawaito wadannan riwayoyi.

 

Yin adalci a tsakanin iyalai yana inganta tarbiyya, yana sanyawa su ji tausayin Uba bayan ya girma,

yana kara musu hadin kai da son juna. Ya

wajaba mazaje su Sani cewa : zagin matayansu

ya sabawa ka’idojin sharia, kuma hanya ce ta

tabarbarewar tarbiyya, domin Yaran za su rabu

biyu, wasu suna bayan mahaifinsu, wasu kuma

Babarsu za su ga ta yi daidai. Ya wajaba a

tausasa harshe lokacin da za’a yi magana da

mahaifi saboda Allah ya hana fadawa Uba kalma

mara kyau ko yaya take, kamar yadda ya zo a

Suratul Isra’i.

 

Allah ne mafi sani.

 

Ba’a son ana

yın muguwar addu’a ga iyalai saboda in aka

dace da lokacin amsar addu’a za ta zamar

masa matsala, kamar yadda ya tabbata a

hadisin Muslim mai lamba ta: 3014.

 

Amsawa:

Dr Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

34. TAMBAYA

BA’A SON DABARA WAJAN FITAR DA ZAKKA!

 

Assalamu Alaikum

 Malam Tambaya ce daga wata ‘yar

uwa kamar haka: “Akwai Marayu a karkashi

na,kuma dukiyarsu tana tare dani,ina ririta musu

bana son taba ta,musamman asalin dukiyar.

Yanzu haka sai iyayena suka nemi na bawa

daya daga cikin ‘yan uwa rancen kudi don yaja

Jari. Yanzu haka an fitar da Zakkah daga kudin

marayun,shine nake so na bashi amma ba bashi

ba. Sai dai in nace Zakkah ce, to su iyaye na ba

za su fahimci dole ne ko an sami hasara dole

ne a fitar da zakkah ba,zasu kara tattaro

matsaloli suce a bada kudi akansu.

Shin ina iya

bashi kudin ba tare da nace Zakkah bace,

la’akari da matsalolin da fadar Zakkar ce zai

jawo min???? Allah ya karawa Malam ilimi da

ikhlasi.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

 To ‘yar’uwa Allah madaukaki ya

yi umarni da kiyaye dukiyar maraya, da kuma

hana cinta, in ba da gwargwadon bukata ba, ga

wanda yake talaka, kamar yadda ayoyin farko-

farkon suratunnisa’i suka tabbatar da hakan. Ba

shi daga cikin sharadin zakka, sai an sanar da

wanda aka bawa cewa zakka ce, kamar yadda

Ibnu Khudamah ya yi bayanin hakan a littafinsa

Al-mugni 2\508 da kuma Annawawy a littafinsa

Al-majmu’u 6\233, don haka in kika bawa fakiri

da niyyar kin fitar da zakka ko da ba ki sanar dashi ba ta yi. Saidai malamai sun hana yin

dabara wajan bada zakka, kamar ya zama kana

so ka yi ma mutum kyauta, amma maimakon ka

dauki kudinka ka ba shi sai rowa ta hana ka, sai

ka yi dabara ka ba shi zakkar da ka yi niyyar

fitarwa. Duk mutumin da ya bayar da zakka

yadda Allah ya yi umarni, tabbas Allah zai

mayar masa da ninkin-ba-ninki.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

35. TAMBAYA

BAWA MAKUSANTA ZAKKA, A MAIMAKON KYAUTA!

 

Assalamu Alaikum,

malam yaya matsayin

mutumin da yake baiwa yan uwansa KYAUTA

duk shekara kafin dukiyarsa ta isa ZAKKA? Da

dukiyarsa ta isa zakka kuma sai ya janye

kyautar shekara da yake basu ya fara basu

ZAKKA? Wannan zakkar ta inganta kuwa?.

Mungode.

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To dan’uwa Allah yana kallon

niyyar mutum ne a duk lokacin da ya aikata aiki,

kamar yadda hakan ya tabbata a hadisai, don

haka in har ba dabara ya yi nufi a zakkarsa ba,

to ta yı, mutukar makusantan suna cikin

wadanda suka cancanci su ci zakka. Annabi

S.a.w. yana cewa : “Yın sadaka ga miskini

sadaka ce kawai, amma yin sadaka ga

makusanci, to sadaka ce da zumunci”, kamar

yadda Tirmizi ya rawaito kuma ya kyautata shi

a hadisi mai lamba ta: 658 a Littafinsa na

Sunan. Niyya ita ce kashin bayan kowanne aiki,

za ta iya gyara shi, ko ta bata shi ko ta daidaita shi.

 

Allah ne mafi Sani

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

21/12/2016

 

36. TAMBAYA

ADDU'AR  ZIYARAR MAKABARTA?

 

Assalamu alaikum  Malam wacce addua'a mamaci yafi bukata ? ko kuma Idan an ziyarci kabarin sa wacce addu'a za'a masa ?

 

Amsa

Wa alaikum as salam,

 Annabi saw ya shar'anta ziyarar makabarta saboda tana tuna lahira, kamar yadda Abu-dawud ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 3237, kuma Albani ya inganta shi.

In mutum ya je kabari an shar'anta ya fadi wannan adduar :

 

السلام عليكم أهل الديار من المؤمنين  والمسلمين، وإنا إن شاء الله  للاحقون، أسأل الله لنا ولكم العافية.

Assalamu alaikum Ahlad diyaar minal Mu'umineena wal Muslimeena, wa innaa insha Allahu La laahiquuna, as'alullaha lanaa wa lakumul 'aafiyah, Muslim a hadisi mai lamba ta : 2302.

 

Allah ne mafi sani

Amsawa

Dr.  JAMILU YUSUF ZAREWA

(04/11/2015)

 

37. TAMBAYA

SIFFOFIN ABOKI NAGARI!

 

Assslamu alaikum Malam ina da abokai da yawa, amma ina so ka ba ni shawara?

 

Amsa

Wa alaikum assalamTo dan'uwa Aboki yana da mutukar mahimmanci a rayuwar mutum, idan ya zama abokinka mutum ne mai himma, sai kai ma ka samu himma kamar yadda ake cewa zama da madaukin kanwa yana kawo farin kai, haka nan idan ya zama mutumin banza sai ya yi maka tasiri, Abu Musa Al’ash’ari ya rawaito hadisi daga Annabi ((s.aw.)) yana cewa (misalin aboki na gari da abokin banza, kamar misalin mai daukar turare ne da mai hura zuga-zugi, mai daukar turare ko dai ya shafa maka ko ka sayi turare a wurinsa ko kuma ka ji kamshi mai dadi a wurinsa, mai hura zuga- zugi kuma ko ya kona maka kaya ko ka ji wari a wurinsa) Bukhari ne ya rawaito

Kuma wani malami yana cewa:

• idan ka kasance a cikin mutane, to ka yi abota da zababbensu, kada ka yi abota da halakakke saiku halaka tare.

• Idan kana so ka san waye mutum, to ka tambayi abokinsa, saboda kowanne aboki da abokinsa yake koyi .

Wani kuma yana cewa:

• Kar ka aboci malalaci a kowanne hali, da yawa mutumin kirki yana lalacewa ne idan ya hadu da mara kirki.

• Dakiki yana saurin tasiri akan mai kokari, ba ka ganin garwashe idan aka saka shi a toka shi ma sai ya zama toka.

Da fatan za ka kula da abin da ya gabata.

Allah na mafi sani

Amsawa

Dr. JAMILY YUSUF ZAREWA

11/11/2017

 

38. TAMBAYA

ZAN IYA RANTSUWA DA AL-QUR'ANI?*

 

Salamun alaikum Dr. Don Allah mene ne hukuncin rantsuwa da Al-Qur'ani?, kamar ka ce: Alquran.

Allah Ya kara ma Dr. Lafiya Amin.

 

AMSA

Wa alaukum assalam, Ya halatta mana tun da qur'ani sifa ne daga cikin sifofin Allah .

 

Annabi S.A.W. Yana cewa: "Duk wanda zai yi rantsuwa, to ya rantse da Allah ko kuma ya yi shiru" kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: (6270).

 

Rantsuwa da Allah ya kunshi rantsewa da daya daga cikin sunayanSa ko daya daga cikin sifofinSa, kamar yadda malamai suka yi bayani.

 

 kasancewar daga cikin sifofin Allah akwai zance,  kuma Al-Qur'ani maganar Allah ce ba halittarsa ba, hakan sai ya halatta rantsuwa da shi.

 

Allah mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

09/11/2017.

 

39. TAMBAYA

BANA SHA’AWAR MATA SAI MAZA IRINA,MENENE MAFITA ?

 

Assalamu Alaikum.

Mallam inada tambaya kuma zan ji

dadi idan za’a iya amsa mun. Mallam mutun ne

balagagge namiji, tun lokacin da ya malliki

hankalin shi yasan cewa yana cikin matsala,

amma ya rasa inda zai danganta

matsalan…sabode ya daure masa kai. Bai taba

kawo son mace a zuciyan shi ba ko sau daya,

baya taba sha’awar mace illa namiji kamar

shi…wannan ba sabode yana kallon batsa bane

ko kuma yana tare da marasa imanin mutane

ba…a’a tun yana karami ake fada masa, cewa

yakan daukan dankwali ya daura, yanayin sa ma

kamar mace yake yi…muryan shi ma idan ba

kasan shi sosai ba sai ka dauka mace ce

magana, abun yana damun sa sosai, ya kai ga

idan yayi barci yayi mafarki da maza yake yi

wato saduwa har maniyyi ya fita. Toh mallam

yanzu ya rasa yadda zai sa kanshi..wannan

wace irin matsala ce? Kuma wani hanya za a bi

wajen samun shifa’a?

 

Amsa

Wa'alaykumussalam

To dan’uwa tabbas ka hadu da babbar musiba, sai dai akwai shawarwari da nasihu kamar haka :

 

1. Ka rinka

yawaita istigfari, saboda yana warware matsaloli,

sannan sha’awar maza tana kaiwa zuwa ga

luwadi, Allah ya hallakar da al’uma kacokan

saboda suna aikata luwadi.

 

2. Ka dinga yawaita addu’a a lokutan da ake amsar roko, kamar cikin

sujjada da karshen dare, saboda Allah zai iya

karbar kukanka, ya kare ka daga wannan fitinar.

 

3. Duk lokacin da tunanin namiji ya zo maka a

zuciya ka yi kokari wajan kautar da tunanin

zuwa wani abu daban mai amfani.

 

4.Shagaltuwa da ayyukan alkairi na taimakawa

wajan kaucewa Alfasha.

 

5. Tuna azabar Allah da

girmansa, suna taimakawa wajan barin sabo.

 

6.Kada ka dinga kwanciya bacci, sai lokacin da ka

tabbatar kana jin bacci, saboda tunane-tunane

suna yawan zuwa a wannan lokacin.

 

7. Nisantar

abokan banza yana gyara halaye.

 

8. Nisantar

cakuduwa da maza zai taimaka maka wajan

rashin sanya su a rai.

 

9. Yawaita karatun

Alqur’ani na nisanta mutum daga shaidanu,

wadanda suke juya dabi’ar mutum.

 

10. Zai yi

kyau in yana da hali ya je wajan kwararrun

llikitoci, saboda za su iya ba shi gudunmawa.

Tare da cewa akwai mutanen da Allah yake

halitta suna da siffofin mata saidai ya wajaba ka

yi iya bakin kokarinka wajan nisantar

kamanceceniya da mata, saboda Annabi s.a.w.

ya la’anci namijin da yake kamanceceniya da

mata, a hadisi mai lamba ta :5546 a Sahihul

Bukhari, sifar da ka yi iya bakin kokarinka ta ki

canzuwa, to Allah ba ya dorawa rai sama da

abin da za ta iya, kamar yadda aya ta karshe a

suratu Bakara take nuni zuwa hakan.

 

Allah ne mafi sani.

Amsawa:

Dr. Jamilu Zarewa

18/12/2016

 

40. TAMBAYA

NA GA WANDONA A JIKE BAYAN NA KAMMALA SALLAH?

 

 Aslamualaikum MALAM na tashi da janaba nayi salar asuba da azahar da kuma laasar, duk nayi sallah sai bayen naje wanka da yemma naga wando na da alamun manniyi shin ya ingancin sallolina na baya ? nagode

 

Amsa

Wa alaikum assalam, mutukar ka tabbatar a baccin asuba maniyyin ya fito, to ya wajaba ka sake asuba da azahar da la'asar din.

 

In har ka yi wani baccin bayan azahar to za ka danganta janabar ne zuwa ga baccin karshe da ka yi, ta yadda sallar da ka yi bayan baccin karshe ita za ka sake, kamar yadda Imamu Malik ya rawaito a Muwadda daga Sayyady Umar.

Allah ne mafi sani

 

Amsawa:

Dr. JAMILU YUSUF ZAREWA

13/11/2017


No comments: